Aminiya:
2025-03-03@09:18:51 GMT

Ɗan Ibo ya yi lalata da ’yan firamare biyu a Zariya

Published: 31st, January 2025 GMT

Ana zargin wani ɗan ƙabilar Ibo mai suna Oguchwku da yin lalata yaran makarantar Firamare masu shekaru 9 da 10 da haihuwa, kuma ‘ya’yan Hausawa ne.

Aminiya ta bibiyi lamarin a inda ta garzaya Cibiyar Kula da cin zarafin mata da ƙananan yara da ke Asibitin Gambo Sawaba Ƙofar Gayan Zariya a Jihar Kaduna.

Shekara 18 aikin Asibitin Sabuwar Kaduna na tafiyar hawainiya Tankar fetur ta yi bindiga a gidan mai Jigawa

Daraktan cibiyar Salama Centre da ke Asibitin Gambo Sawaba ƙofar Gayan Zariya, Hajiya Aishatu Ahmad, ta shaida wa Wakilin namu cewar a ranar 27 ga watan ɗaya na wannan shekarar ne hukumar ‘yan sanda da ke Kasuwar Mata a ƙaramar hukumar Sabon Gari ta kawo wani mai suna Oguchwku Cibiyarsu tare da wasu yaran Makarantar Firamare ta Jafaru LEA su biyu.

Daraktar ta ce, bayan kammala binciken yaran, bincike ya nuna cewa an yi lalata da su.

Daraktan cibiyar Hajiya Aishatu Ahmad ta ce, sun ɗora yaran akan magani, kuma sun ba ‘yan sanda sakamakon, tare da tura ƙwafin sakamakon zuwa ga Kwamishinan jinƙai da walwala ta jihar Kaduna domin ɗaukar mataki.

Babban jami’I a ofishin ‘yan sanda na Kasuwar Mata ya ce duk da taƙardama akan rashin yarda da sakamakon binciken da Asibitin Gambo Sawaba da iyalan wadda ake zargin suka yi sai na sake tura su asibitinmu na musamman domin ƙara binciken kuma yanzu haka mun tura su zuwa Kaduna.

Duk ƙoƙarin kiran wayar, mai magana da yawan rundunar ‘yan sanda jihar Kaduna ASP Mansur Hassan, tare da tora saƙon karta kwana amma har zuwa wannan lokacin bai amsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: firamare Zaria

এছাড়াও পড়ুন:

Fasinjoji 12 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Edo

Aƙalla fasinjoji 12 ne suka ƙone ƙurmus har lahira a wani mummunan hatsari da ya auku a kan titin Benin zuwa Auchi a Jihar Edo.

Kakakin Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC) a Edo, Cyril Mathew, ya tabbatar da aukuwar hatsarin.

Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a Bauchi Abubuwan da ya kamata a sani game da azumin watan Ramadana

Ya ce wata mota ƙirar Toyota Hiace ce ta yi karo da babbar tifa.

A cewarsa, hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5 na asuba a ranar Asabar, a kusa da wani shingen sojoji da ke yankin Igueoviobo.

“Motar ta taso ne daga Zuba a Babban Birnin Tarayya tana kan hanyarta n zuwa Benin, amma ta yi karo da wata babbar tifa da ke kan hanyar zuwa Auchi.

“Duk fasinjojin da ke cikin motar sun rasa rayukansu,” in ji shi.

Mathew, ya ce ana zargin direban motar da gajiya yayin tuƙi, lamarin da ya sa ya fara barci a kan hanya, wanda hakan ya haddasa hatsarin.

Karon da motocin suka yi ya haddasa tashin wuta, lamarin da ya sanya fasinjojin zuka ƙone ƙurmus.

Sai dai direban babbar tifar da yaronsa sun tsira ba tare da sun ji rauni ba.

Kakakin ya shawarci direbobi da suke hutawa a duk lokacin da suka gaji domin gujewa aukuwar hatsari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɓacewar bindigogi 4,000: Sakaci ne dalili —’Yan sanda
  • Fasinjoji 12 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Edo
  • Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a Bauchi
  • Zargin Neman Yin Lalata: Ina Da Kwararan Hujjoji Akan Akpabio – Natasha 
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Malaman Furanare 116 Sun Gabatar da Addu’o’i a Zaria
  • Ramadan: ’Yan sanda sun tsaurara tsaro saboda azumi a Borno
  • Gobara ta ƙone sashen wani asibiti a Legas
  • Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu
  • Hukumar Alhazai Ta Kaduna Ta Nemi Goyon Bayan Sarkin Zazzau Don Nasarar Aikin Hajjin Bana