Leadership News Hausa:
2025-03-03@21:22:21 GMT

Rikicin Shugabanci Na Barazana Ga Babban Taron Jam’iyyar PDP

Published: 31st, January 2025 GMT

Rikicin Shugabanci Na Barazana Ga Babban Taron Jam’iyyar PDP

An yi kokarin cire Damagum ta hanyoyin siyasa, ciki har da yiwuwar nada sabon shugaba daga yankin arewa ta tsakiya, amma hakan ya ci tura.

Gwagwarmayar bangaranci dai ta kara dagula al’amuran cikin gida na jam’iyyar, inda aka samu bangaren masu biyayya ga fitattun mutane irin su tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike.

Wadannan rarrabuwar kawuna sun gaza samar da fahimtar juna, wadanda suka zama kalubalen da ya haifar da dakatarwar wasu daga cikin jami’an jam’iyyar.

Yayin da watan Fabrairun 2025 ke gabatowa, masu ruwa da tsaki sun nuna damuwarsu na cewa PDP na fuskantar babban kalubale a gabanta.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NLC ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki

Ƙungiyar Kwadago ta Nijeriya, NLC, ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin wutar lantarki a daidai lokacin da ’yan ƙasar ke fama da ƙuncin rayuwa.

NLC ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta dakatar da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki da masu amfani da layin A da B da C.

Hakar ma’adanai: ILO ta horas da masu ruwa da tsaki kan illar bautar da yara Miji ya amince saurayin matarsa ya tare a gidansu

Channels TV ya ruwaito wannan daga sanarwa da NLC ɗin ta fitar a ranar Lahadi bayan wani taro da ta yi a Jihar Adamawa.

“NLC ba ta amince da yunƙurin Hukumar Lantarki ta Nijeriya NERC na ƙoƙarin sauya layin lantarkin kwastomomi daga layin B da A da sunan haɓaka samun lantarki ba, alhali kuma yunƙuri ne kawai na ƙara wa mutane kuɗin wuta ba tare da sun shirya ba,” in ji sanarwar.

“Ya bayyana ƙarara cewa dai yanzu masu ƙarfi a ƙasar na ƙara jefa marasa ƙarfi cikin ƙunci ta hanyar ƙara kuɗin haraji da lantarki da sauransu a daidai lokacin da tattalin arzikin ƙasar ya tsaya cak.”

Ƙungiyar ta ƙara da cewa ba za ta lamunci ƙarin kuɗin wutar ba, inda ta yi barazanar shirya zanga-zanga a faɗin ƙasar.

A makon jiye ne dai Ministan Lantarki, Adebayo Adelabu, ya sanar da cewa za a mayar da masu amfani da lantarki a layin Band C da B zuwa layin A.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar CPPCC Za Ta Gudanar Da Taron Shekara-shekara Daga Ranar 4 Zuwa Ta 10 Ga Maris
  • Tawagar ECOWAS Ta Fice Daga Guinea-Bissau Bayan Barazana Daga Shugaban Kasar
  • NLC ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki
  • Za A Gudanar Da Taron Manema Labarai Na Taro Na Uku Na NPC Karo Na 14 A Ranar 4 Ga Maris
  • Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan
  • HKI Ta Yi Barazanar Shiga Rikicin Da Ya Barke  A Garin Jarmana Na Kasar Syria
  • Xi Ya Jaddada Ciyar Da Shirin Kasar Sin Mai Kwanciyar Hankali Zuwa Babban Mataki
  • A Yau Ce Dokar Haramta Amfani Da Tankunan Mai Masu Daukar Lita 60,000 A Najeriya
  • Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu
  • Taron Kara Wa Juna Sani Kan Canton Fair Ya Ja Hankalin Masu Masana’antu Da ‘Yan Kasuwan Habasha