Aminiya:
2025-04-02@12:38:46 GMT

Zaftarewar ƙasa ta kashe mata masu haƙar zinare a Mali

Published: 31st, January 2025 GMT

Masu haƙar zinare aƙalla mutum 10 sun mutu wasu da dama sun ɓace bayan zaftarewar ƙasa a kansu a wani filin haƙar ma’adinai yankin Koulikokro na ƙasar Mali.

Hukumomin yankin sun bayyana cewa mata ne yawancin masu haƙar zinaren da abin ya rutsa da su mata ne, kuma an kasa ciro gawarwakinau, “saboda tsananin sarƙaƙiyar yanayin.

Gwamnatin yankin ya bayyana cewa ajali ya rutsa da su ne a ƙauyen Danga, a cikin wani rami mai ruwa da laka, wanda zaftarewar ƙasar ta binne su a ciki a ranar Laraba.

Ta bayyana a shafinta na Facebook cewa “abin takaicin shi ne babu ko mutum ɗaya da ya tsira a cikin su.”

Matashi ya yi lalata da ’yan firamare biyu a Zariya Tankar fetur ta yi bindiga a gidan mai Jigawa

Jami’in kula da haƙar ma’adanai a yankin, Ousmane Diakite, ya bayyana cewa, “akalla mutum 10 ne abin ya yi alajinsu.”

Wani jami’in gwamnati da ya nemi a bole sunansa ya bayyana wa  kamfanin dillancin labarai na AFP cewa akwai yiwuwar adadin zai karu, a yayin da hukumomi ake ci gaba aikin ceto.

Magajin wani gari da ke maƙwabtaka da Koulikokro, ya bayyana wa AFP cewa, “babu wanda ya tsira bayan faruwar lamarin.”

Mali na daga cikin ƙasashe mafiya talauci a duniya, duk da cewa tana cikin ƙasashen mafiya arzikin zinare a nahiyar Afirka.

Zaftarewar ƙasa na yawan halaka masu haƙar zinare a ƙasar, a yayin da hukumomi ƙasar ko ƙoƙarin kawo ƙarshen amfani da hanyoyin gargajiya wajen gudanar da harkar.

A watan Janairun 2024 zaftarewar ƙasa ta kashe masu halartar zinare 70 a wurin da na ranar Larabar nan ya faru.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: haƙar zinare masu haƙar zinare

এছাড়াও পড়ুন:

Talakawa su girmama shugabanni yayin bayyana matsalolinsu — Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su guji cin mutuncin shugabanni yayin da suke bayyana matsalolinsu, inda ya jaddada cewa girmamawa da ladabi suna fi tasiri wajen samun mafita.

“Idan ka zagi shugabanka, ta yaya kake so ya taimaka maka?” in ji shi.

Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta Abubuwan da ya kamata Musulmi ya yi a ranar Karamar Sallah

“Amma idan ka yi magana da ladabi, zai saurare ka kuma ya ɗauki mataki.”

Da yake jawabi bayan sallar Idi a Sakkwato, Sarkin Musulmi, ya buƙaci ’yan Najeriya da su ci gaba da yi wa shugabanni addu’a da kuma zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

“Ku yi wa Shugaban Ƙasa, Gwamnoni da sauran shugabanni addu’a domin Allah Ya ba su ikon sauke nauyin da ke kansu,” in ji shi.

Ya taya Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan tare da yin kira da su ci gaba da koyi da halaye nagari da suka koya a cikin wata mai alfarma.

Hakazalika, ya jinjina wa malamai kan yadda suka gudanar da wa’azin Ramadan cikin hikima, tare da buƙatar su ci gaba da yaɗa zaman lafiya da haɗin kai a cikin al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muna samun galabar daƙile kwararowar baƙin haure — Jamus
  • Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha
  • Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha
  • Girgizar Ƙasa: Mutum 1,700 Sun Rasu, 3,400 Sun Jikkata A Myanmar
  • Gwamna Abba Ya Nemi A Bayyana Fuskokin Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Tsawa Ta Kashe Makiyayi Da Shanu A Kudancin Kaduna
  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  • Talakawa su girmama shugabanni yayin bayyana matsalolinsu — Sarkin Musulmi