Aminiya:
2025-04-25@02:29:17 GMT

Zaftarewar ƙasa ta kashe mata masu haƙar zinare a Mali

Published: 31st, January 2025 GMT

Masu haƙar zinare aƙalla mutum 10 sun mutu wasu da dama sun ɓace bayan zaftarewar ƙasa a kansu a wani filin haƙar ma’adinai yankin Koulikokro na ƙasar Mali.

Hukumomin yankin sun bayyana cewa mata ne yawancin masu haƙar zinaren da abin ya rutsa da su mata ne, kuma an kasa ciro gawarwakinau, “saboda tsananin sarƙaƙiyar yanayin.

Gwamnatin yankin ya bayyana cewa ajali ya rutsa da su ne a ƙauyen Danga, a cikin wani rami mai ruwa da laka, wanda zaftarewar ƙasar ta binne su a ciki a ranar Laraba.

Ta bayyana a shafinta na Facebook cewa “abin takaicin shi ne babu ko mutum ɗaya da ya tsira a cikin su.”

Matashi ya yi lalata da ’yan firamare biyu a Zariya Tankar fetur ta yi bindiga a gidan mai Jigawa

Jami’in kula da haƙar ma’adanai a yankin, Ousmane Diakite, ya bayyana cewa, “akalla mutum 10 ne abin ya yi alajinsu.”

Wani jami’in gwamnati da ya nemi a bole sunansa ya bayyana wa  kamfanin dillancin labarai na AFP cewa akwai yiwuwar adadin zai karu, a yayin da hukumomi ake ci gaba aikin ceto.

Magajin wani gari da ke maƙwabtaka da Koulikokro, ya bayyana wa AFP cewa, “babu wanda ya tsira bayan faruwar lamarin.”

Mali na daga cikin ƙasashe mafiya talauci a duniya, duk da cewa tana cikin ƙasashen mafiya arzikin zinare a nahiyar Afirka.

Zaftarewar ƙasa na yawan halaka masu haƙar zinare a ƙasar, a yayin da hukumomi ƙasar ko ƙoƙarin kawo ƙarshen amfani da hanyoyin gargajiya wajen gudanar da harkar.

A watan Janairun 2024 zaftarewar ƙasa ta kashe masu halartar zinare 70 a wurin da na ranar Larabar nan ya faru.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: haƙar zinare masu haƙar zinare

এছাড়াও পড়ুন:

An kama wasu mata na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace

Rundunar ’yan sandan Jihar Imo ta kama wasu mata biyu a lokacin da suke yunƙurin sayar da wani yaro ɗan shekara huɗu da aka yi garkuwa da shi a Owerri kan kuɗi Naira miliyan 2.7.

An yi garkuwa da yaron ne a Abuja a lokacin da yake tallan kayan miya, sannan aka kawo shi Owerri a sayar da shi kafin a sa’ar kuɓutar da shi daga masu son sayar da shi.

An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji

Waɗanda ake zargin sun haɗa da Joy Ugwu daga garin Idah ta jihar Kogi, da Rosella Michael daga garin  Zamba da ke Abuja, yayin da ta ukun da ake zargin ma’aikaciyar jinya ce da ta tsere a yanzu.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Henry Okoye ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

Okoye ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a Owerri, babban birnin jihar a ranar 14 ga watan Afrilu, biyo bayan wani samame da jami’an tsaro suka yi a lokacin da suke ƙoƙarin siyar da yaron kan kuɗi Naira miliyan 2.7.

Ya ce, an kama mutanen ne biyo bayan ƙoƙarin haɗin gwiwa tsakanin rundunar ’yan sandan Jihar Imo da hedikwatar ’yan sandan shiyya ta 7 da ke Abuja, duk da cewa an miƙa waɗanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na shiyyar Abuja, domin ci gaba da bincike da gurfanar da su gaban kuliya.

Okoye ya ce, “Rundunar ’yan sandan Jihar Imo ta gano wani mutum da ake zargi da safarar ƙananan yara, lamarin da ya kai ga cafke wasu mata biyu da ake zargi tare da kuɓutar da wani yaro ɗan shekara huɗu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Ministan Tsaron Pakistan Ya Yi Wa Pakistan Barazanar Kai Mata Hari Mai  Tsanani
  • An kama wasu mata na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 47 A Birnin El-Fasher Fadar Mulkin Darfur Ta Arewa
  • Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe
  •  WHO: Masu Ciwon Koda 400 A Gaza Sun Mutu Saboda Rashin Magani
  • Rage Mace-Macen Mata Da Jarirai: Kasar Sin Ta Ba Da Kyakkyawan Misali Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Kotu A Kano Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wani Matashi Da Ya Kashe Ƙanwarsa Da Kishiyar Mahaifiyarsa
  • ECOWAS Zata YI Taro A Ghana Don Tattauna Batun Niger, Mali Da Burkina Faso
  • Gwamna ya dakatar da basarake kan satar mutane da yankinsa