Ya tona kabarin mijin mahaifiyarsa ya yanke kansa a Adamawa
Published: 31st, January 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Adamawa ta kama wani mafarauci mai shekara 55 mai suna Yusuf Garba wanda aka fi sani da Gana kan zarginsa da tona kabari tare da yanke kan mijin mahaifiyarsa.
A cewar jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, SP Suleiman Yahaya Nguroje, wanda ake zargin ya amsa laifinsa ne a lokacin da ake masa tambayoyi.
Garba wanda ɗan asalin garin Tappare Kona Uku ne a ƙaramar hukumar Jada ta jihar, ya bayyana cewa ɗan marigayin ne ya tuntuɓe shi inda ya buƙaci kan mijin mahaifiyarsa don yin tsafi bayan rasuwarsa.
Shekara guda bayan binne shi, ɗan ya dawo ya nemi kan mijin mahaifiyarsa don yin tsafin al’adun gargajiya.
Garba ya yi iƙirarin cewa ɗan mijin mahaifiyarsa ne ya matsa masa lamba, wanda ya yi imanin matsafi ne kuma zai iya cutar da shi ko kuma ‘ya’yansa idan ya ƙi bin umarninsa.
Ya ce, “Na ɗauki fartanya da misalin ƙarfe 4:00 na asubahi, na je maƙabarta, na tona kabari, na yanke kan sa.
Sai ya dawo gida ya ba wa yaron kan a cikin jakar leda.
Wanda ake zargin ya ci gaba da bayanin cewa bayan mako biyu, matar marigayin ta zo wurinsa inda ta shaida masa cewa ta yi munanan mafarki tun lokacin da aka ajiye kan a ɗakin kwanansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa kabari mijin mahaifiyarsa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16
Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, ya kai ziyara ga Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, domin nuna alhini kan kisan gilla da aka yi wa matafiya dyan Arewa a Uromi. Harin da aka kai a ranar Alhamis ya haifar da mutuwar mafarauta da ke kan hanyar zuwa bikin Sallah. Gwamnan ya bayyana cewa an kama mutane 14 da ake zargi da hannu a kisan, kuma za a kai su Abuja domin ci gaba da bincike.
A yayin ziyarar, Gwamnan Okpebholo ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta taimaka wa iyalan wadanda aka kashe, yana mai nuni da cewa Shugaban kasa da Yansanda sun dauki matakai kan lamarin. “Za mu tabbatar an gurfanar da wadanda suka aikata wannan mugun aiki a gaban doka,” in ji Gwamnan. Sanata Barau ya amsa da yabon matakan gwamnatin Edo, yana mai cewa: “Dole ne a ci gaba da yin Adalci domin hana irin wannan bala’i a nan gaba.”
Yadda ‘Yan Banga A Edo Suka Yi Sanadin Kashe Matafiya Mafarauta 16 – Direban Motar YANZU-YANZU: Gwamnan Edo Ya Kai Ziyarar Jaje Kan Kisan Mafarauta A Uromi‘Yansandan sun kara da cewa za su ci gaba da yaki da duk wani yunkurin tayar da tarzoma a jihar. Gwamnan Edo ya kuma yi kira ga al’umma da su yi haƙuri, yana mai jaddada cewa jihar ba ta yarda da ‘yan daba ko dakar doka a hannu ba. “Edo ta kasance gida ne na zaman lafiya ga dukkan al’ummar Nijeriya, kuma za mu kiyaye wannan tarihi,” in ji Gwamnan
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp