Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugabannin Hamas A Ziyararsa Doha
Published: 31st, January 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da ke ziyara a Qatar ya gana da shugabannin Hamas a inda suka tattauna batun sake gina Gaza.
Tattaunawar a birnin Doha ta hada fitattun jami’an kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da suka hada da Mohammed Darwish shugaban majalisar tuntuba ta Shura da Khalil al-Hayya babban mai shiga tsakani na kungiyar.
A yayin ganawar, Darwish ya bayyana Operation Al-Aqsa Storm a matsayin wani sabon salo a gwagwarmayar da al’ummar Palastinu ke yi da gwamnatin mamaya.
Ya jaddada cewa yunkurin gwamnatin Isra’ila na raba al’ummar Falasdinu da kasarsu ta hanyar yakin kisan kare dangi da sauran hanyoyi ya ci tura.
Ya nanata cewa al’ummar Falastinu sun ci gaba da dagewa wajen kare hakkinsu da kuma wurare masu tsarki na kasarsu ciki har da masallacin Al-Aqsa.
A nasa banagre ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya jaddada irin goyon bayan da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take ba wa gwagwarmayar al’ummar Palastinu, sannan ya yaba da irin jaruntakar da al’ummar Gaza suka yi, lamarin da ya ce ya tona a fili gazawar gwamnatin Isra’ila.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
‘Fake Inbestment Schemes’: Masu cuta na amfani da shafukan zuba jari na bogi domin damfarar mutane.
Ransomware: Wasu barayin yanar gizo na saka kwayoyin cutar kwamfuta domin su hana mutum amfani da na’urarsa sai ya biya kudi.
Hanyoyin Kare Kanka
Yi amfani da kwayoyin kalmomin sirri masu karfi – A guji amfani da kalmomin sirri kamar sunanka ko shekarunka.
Yi amfani da Two-Factor Authentication (2FA) – Wannan yana 1ara kariya ga asusunka.
Guji danna hadin gwiwa (links) daga tushe da ba a san su ba – Yawancin wadannan hanyoyin suna da cutarwa.
Ka tabbata cewa shafin da kake ziyarta yana da alamar ‘https’ – Wannan yana nuna cewa shafin yana da kariya.
Kar ka raba bayanan sirrinka da kowa – Kar a taba bayar da PIN, OTP, ko wasu muhimman bayanai.
Labari Mai Karfafa Gwiwa
Akwai wata mata mai suna Zainab wacce ta samu sako daga wani wanda ya ce ta ci kyautar N500,000. Da yake tana da ilimi a kan Phishing, ta lura cewa sakon yana da alamun yaudara. Ta guji danna link da aka tura mata kuma ta sanar da abokanta domin su kare kansu. Wannan yana nuna cewa sanin dabarun kare kai a intanet yana da matukar muhimmanci.
Kammalawa
A duniyar intanet, dole ne kowa ya kasance cikin shiri domin guje wa damfarar yanar gizo. Mu kasance masu taka-tsantsan da duk wani bayani da muke rabawa a intanet. Kada mu yarda da komai da muke gani online sai mun tabbatar da gaskiyarsa.
Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp