HausaTv:
2025-04-23@01:40:22 GMT

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugabannin Hamas A Ziyararsa Doha

Published: 31st, January 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da ke ziyara a Qatar ya gana da shugabannin Hamas a inda suka tattauna batun sake gina Gaza.

Tattaunawar a birnin Doha ta hada fitattun jami’an kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da suka hada da Mohammed Darwish shugaban majalisar tuntuba ta Shura da Khalil al-Hayya babban mai shiga tsakani na kungiyar.

A yayin ganawar, Darwish ya bayyana Operation Al-Aqsa Storm a matsayin wani sabon salo a gwagwarmayar da al’ummar Palastinu ke yi da gwamnatin mamaya.

Ya jaddada cewa yunkurin gwamnatin Isra’ila na raba al’ummar Falasdinu da kasarsu ta hanyar yakin kisan kare dangi da sauran hanyoyi ya ci tura.

Ya nanata cewa al’ummar Falastinu sun ci gaba da dagewa wajen kare hakkinsu da kuma wurare masu tsarki na kasarsu ciki har da masallacin Al-Aqsa.

A nasa banagre ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya jaddada irin goyon bayan da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take ba wa gwagwarmayar al’ummar Palastinu, sannan ya yaba da irin jaruntakar da al’ummar Gaza suka yi, lamarin da ya ce ya tona a fili gazawar gwamnatin Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Zata Gudanar Da Tarin Kare Hakkin Bil’adama Ta Faskar Gabacin Duniya A Karo Na Farko

Shugaban hukumar al-adun musulunci da sadarwa a nan Iran Mohammad Mehdi Imamipour ya bayyana cewa za’a gudanar da taron kasa da kasa na kare hakkin bil’adama a karon farko a nan kasar Iran tare da mahangar kasashen gabas.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Imanipour yana fadar haka a yau, ya kuma kara da cewa za’a bude tarurrukan ne a nan birnin Tehran, Qom da kuma Esfahan a lokaci guda daga ranar 28 ga watan Afrilu zuwa 2 ga watan mayu.

Labarin ya ce matsalar kare hakkin bil’adama yana daga cikin al-amuran da ake nuna faska biyu a cikin al-amura da dama a duniya, musamman kan abinda yake faruwa a kasar. Imanipour y ace suna son gudanar da taron ko wani shekaru 4.

Ya zuwa yanzu dai inji shi, an gayyaci masana da kwararru daga kasashe 32 a duniya. Sannan an karbi rubuce-rubuce har 491, daga ciki 186 daga Amurka, Austria, Masart, Kenya, Tunisia, Rasha, China, Kazakhstan, Indonesia, Lebanon, Malaysia, Iraq, Nigeria, Serbia, Espaniya da kuma Netherlands. Har’ila yau tare da 305 daga cikin gida.

Daga karshe yace JMI tana son a samarda wata sabuwar mahanga ta kare hakkin bil’ada a duniya sabanin wadanda kasashen yamma suke jagoranta a halin yanzu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Zata Gudanar Da Tarin Kare Hakkin Bil’adama Ta Faskar Gabacin Duniya A Karo Na Farko
  • Wang Yi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Sabon Ministan Harkokin Wajen Sudan Ta Kudu
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Ministan HarkokinWajen Iran Ya Tattauna Da Takwarorinsa Na Swaitzerland Da Pakistan Ta Wayar Tarho
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam Ta Amnesty International Ta Ce; Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ba Ta Dace Da Bincike Laifukan Sojojinta Ba
  • New York Times : Amurka na son rage ofisoshin jakadncinta a Afirka
  • An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
  • Hamas ta yi watsi da shirin kwance damara na Isra’ila
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma