An Fara Bukukuwan Kwanaki Goma Na Cin Nasarar Juyin Juya Halin Musulinci A Iran
Published: 31st, January 2025 GMT
Al’ummar kasar Iran sun fara gudanar da bukukuwan cika shekaru 46 da juyin juya halin Musulunci na shekara ta 1979, wanda ya kawo karshen mulkin kama karya, wanda ya kai ga kafuwar Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Kamar kowace shekara, ana fara bukukuwan ne da karfe 9:33 na safe, na ranar 1 ga Fabrairu, 1979, ga jirgin saman Air France da ya dawo da Imam Khumaini gida daga gudun hijira na sama da shekaru 14 wanda ya kai ga kafa Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
A yayin bukukuwan al’ummar Iran suna halartar taruka daban-daban har zuwa zagayowar ranar 22 ga watan Bahman wato 10 ga watan Fabrairu, wato ranar tunawa da juyin juya halin Musulunci.
Juyin juya halin Musulunci ba wai kawai ya sake fasalin tsarin siyasar Iran ba ne, har ma ya sake fasalin matsayinsa na duniya, tare da kafa Jamhuriyar Musulunci a matsayin sabuwar hanyar samun ‘yancin kai daga wani yanki na gabas ko na yamma.
Ta hanyar kifar da gwamnatin sarki Shah Pahlavi shekaru 46 da suka gabata, al’ummar Iran sun kawo karshen mulkin shekaru 2,500 na sarauta tare da kafa wani sabon tsarin siyasa jamhuriya mai tushe bisa kimar Musulunci da dimokuradiyya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta kashe yara 322 cikin kwanaki 10 a Gaza — UNICEF
Alƙaluman Asusun Tallafawa Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya UNICEF ya ce Isra’ila ta kashe ƙananan yaran da yawansu ya kai 322 cikin kwanaki 10 da suka gabata a hare-haren da suke ci gaba da kai wa sassan Gaza.
Alƙaluman da UNICEF ta fitar ta ce a jimilla ƙananan yara fiye da dubu 15 ne Isra’ilan ta kashe cikin kusan watanni 18 da ta shafe tana yiwa yankin na Gaza luguden wuta, kuma daga lokacin da ƙasar ta katse yarjejeniyar tsagaita wutar da ke tsakaninta da Hamas ta kashe ƙananan yaran da yawansu ya kai 322 tare da jikkata 609.
Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha Haaland zai yi jinyar mako bakwai — GuardiolaA cewar UNICEF galibin ƙananan yaran da Isra’ila ta kashe, na rayuwa ne a sansanonin wucin gadi bayan da hare-haren ƙasar ya rusa gidajensu tare da tilasta musu barin muhallansu.
Cikin adadin yaran har da tarin waɗanda Isra’ilan ta kashe suna tsaka da bukukuwan Sallah wato a ranar idi da washegari, galibinsu sanye da tufafi da kuma adon sallah kamar yadda hotuna suka nuna.
A cewar UNICEF yanzu haka akwai jumullar ƙananan yara fiye da dubu 34 da Isra’ilan ta jikkata, cikinsu har da waɗanda yanayi ke nuna yiwuwar sai an yanke musu wani sashe na jikinsu, a dai dai lokacin da ake fuskantar ƙarancin alluran kashe raɗaɗin ciwo a zirin na Gaza mai fuskantar ƙawanya.
Wannan alƙaluma na WHO na zuwa a daidai lokacin da Isra’ila ke amsa laifin cewa tabbas sojojinta ne suka buɗe wuta kan motar jami’an agaji kodayake Amurka ta ce laifin Hamas ne.