Leadership News Hausa:
2025-03-03@16:43:03 GMT

Dangantakar Cinikayya Da Sin Ta Budewa Afrika Kofar Samun Ci Gaba

Published: 31st, January 2025 GMT

Dangantakar Cinikayya Da Sin Ta Budewa Afrika Kofar Samun Ci Gaba

An bayyana dangantakar cinikayya tsakanin kasar Sin da Afrika a matsayin wadda ta taimaka wajen gaggauta ci gaba da samar da irin zamanantarwar da nahiyar ke bukata domin ta kasance cikin takara a duniya.

Muya Guo, shugabar sashen Sin a bankin Stanbic na Kenya ne ta bayyana haka yayin wata hira a Nairobin Kenya, inda ta ce dangantakar cinikayya tsakanin Sin da Afrika tare da jarin da kasar ta nahiyar Asiya ke zubawa, sun dora nahiyar kan tafarkin samun ci gaba, yayin da ta zamanantar da muhimman bangarori kamar na kere-keren kayayyaki.

‘Yan Adawa Sun Caccaki Buhari Kan Kalamunsa Na Cewa, ‘Allah Ne Kadai Zai Iya Gyara Nijeriya’ Fatara Da Talauci Na Yi Wa ‘Yan Nijeriya Miliyan 13 Barazanar Fadawa Kangin Talauci A 2025 — Rahoto

A cewarta, makomar dangantakar tattalin arziki tsakanin Sin da Afrika na da haske, wadda ke samun karin kuzari daga jarin da bangarori masu zaman kansu da gwamnatin Sin ke zubawa, tana cewa, za a kara mayar da hankali kan ayyukan da suka shafi bangarorin makamashi da kere-kere da ababen more rayuwa.

Ta kuma bayyana cewa, karin kamfanonin Sin masu kera kayayyaki sun kafa sansanoninsu a kasar Kenya, inda suke daukar mutanen wurin aiki da koyar da fasahohi, lamarin dake bayyana kuzarin dangantakar tattalin arziki dake tsakanin bangarorin biyu. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Somaliya Da Habasha Suna Gab Da Rattaba Hannu Akan Amfani Da Tashar Jirgin Ruwa

Ministan harkokin wajen kasar Ali Muhammad Umar ya bayyana cewa; Somaliya za ta iya  rattaba hannu akan takardun fahimtar juna da za su bai wa Habasha izinin amfani da tashar ruwa da take a gabar tekun Indiya daga nan zuwa watan Yuni.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne dai Fira ministan kasar Habasha Abi Ahmed ya kai ziyara zuwa kasar Somaliya inda ya gana da shugaban kasar Hassan Sheikh Mahmud, kuma bangarorin biyu su ka tattauna hanyoyin bunkasa alaka a tsakanin kasashensu.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Habasha Nebiat Gatachewa ya ce; kokarin da ake yi na bunkasa alaka a tsakanin Addis Ababa da Magadishu ya haifar da da, mai ido musamman a siyasance da kuma ta hanyar diplomasiyya.

Nebiat ya kuma ce; Sabon shafin da aka bude na alakar kasashen biyu yana da alfanu ga kasashen biyu, sannan kuma da samar da zaman lafiya a cikin yankin.

Sabani a tsakanin kasashen biyu masu makwabtaka da juna ya kunno kai ne a shekarar da ta gabata, bayan da kasar ta Habasha ya kulla yarjejeniya da yankin Somaliland akan tashar jirgin ruwa.

Ita dai kasar ta Habasha ba ta da iyaka da ruwa, don haka take son amfani da mashigar ruwan kasar ta yankin Somaliland. Habashan dai tana son gina wani yanki na kasuwanci a gabar ruwan  ta yankin Somaliland.

 Yankin Somaliland na kasar Somaliya ne wanda Mogadishu  take daukar cewa ba kasa ce mai cin gashin kanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya
  • Masar Za Ta Bayyana Shirin Sake Gina Gaza A Yayin Taron Larabawa
  • Kasashen Somaliya Da Habasha Suna Gab Da Rattaba Hannu Akan Amfani Da Tashar Jirgin Ruwa
  • Fitaccen Fim Din Na Kasar Sin Mai Suna “Ne Zha 2” Ya Zama Na 7 A Jerin Fina-finai Mafi Samun Kudi A Duniya
  • Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta
  • Sin Ta Kiyaye Girmama Kasashen Tsibirai Na Yankin Tekun Pasifik
  • An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House
  • Habasha Da Somaliya Sun Tattaunawa Hanyoyin Sake Mayar Da Alaka
  • Rasha Za Ta Bunkasa Kai Wa  Nahiyar Afirka Alkama
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu