’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 24 a Zamfara
Published: 31st, January 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe mutane uku tare da yin garkuwa da wasu 24 a wasu jerin hare-hare a wasu kauyuka hudu a Ƙaramar Hukumar Shinkafi da ke Jihar Zamfara.
’Yan ta’adan sun kai hare-haren ne ranar Alhamis, a ƙauyukan Shinkafi da Jangeru da Shanawa da Birnin Yero.
A garin Shinkafi, ’yan bindigar sun kashe mutum uku tare da yin garkuwa da wasu tara, ciki har da mata hudu.
Mazauna garin sun bayyana cewa maharan sun bude wuta kan mai uwa da wabi, lamarin da ya haifar da fargaba.
Direba cikin barasa ya murƙushe sojoji sun mutu a Legas Ya tona kabarin mijin mahaifiyarsa ya yanke kansaA kauyen Birnin Yero, ’yan bindiga sun kai hari a wani masallaci a lokacin sallar magariba, suka yi awon gaba da mutane takwas tare da raunata wasu da dama wadanda suka tsere zuwa cikin daji.
Sun kuma kai hari kauyen Shanawa, inda suka sace mutane hudu. Wannan harin ya faru ne kwana guda bayan an sako wasu mazauna kauyen guda 12 bayan an biya kudin fansa naira miliyan 12.
A Jangeru, an yi garkuwa da wata mata amma daga baya aka yi watsi da ita a cikin daji bayan da ’yan bindigar sun tabbatar ba za ta iya ci gaba da tafiya ba.
Wani mazaunin garin ya bayyana cewa sun sumar da ita ne, sai daga bisani ta dawo hayyacinta ta koma kauyensu.
’Yan ta’addan sun kuma gargadi mazuna kauyukan Kwari da Kurya, inda suka bai wa mazauna kauyukan wa’adin kwanaki uku su fice daga gidajensu ko kuma su fuskanci farmaki.
Sai dai mazauna kauyen Kurya sun sha alwashin yin fito-na-fito da wannan barazana, inda suka bayyana cewa sun gaji da biyan haraji da kudin fansa.
Sun kuma yi kira ga gwamnati da ta kara yawan jami’an tsaro domin taimaka musu wajen kare kansu daga hare-hare a nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida
Rahotanni da suke fitowa daga Nijar sun bayyana cewa; Wata kungiyar mai alaka da al-ka’ida ta dauki alhakin kashe sojojin kasar 11 a kan iyaka da Aljeriya.
A ranar Juma’ar da ta gabata ne dai lamarin ya faru,kuma a jiya Asabar ne aka yi jana’izarsu a garin Agadez, kamar yadda wata majiyar watsa labara ta jamhuriyar Nijar ta ambata.
Shafin “Air Info” da ya watsa laabrin ya kuma ce; Jami’an soja da dama sun hjalarci jana’izar sojojin da su ka kwanta dama, daga cikinsu har da janar Musa Salih Barmo, babban hafsan hafsoshin sojan kasar.
Tashar Radiyo din kasar ta Nijar ta ce, an yi wa sojojin kwanton bauna ne a lokacin da suke sintiri akan mahadar iyakaokin kasar, da Mali da kuma Burkina Faso.
Labarin Radiyon ya kuma ce, Janar Barmo ya nufi asibitin garin Agadez din domin yin dubiyar sojojin da su ka jikkata.”
A gefe daya wata kungiyar mai suna; “Nasratul-Islam Wal Muslimin” da reshe ne na alka’ida, ta dauki alhakin kai harin.
A lokuta da dama a baya sojojin na jamhuriyar Nijar sun sha fuskantar hare-hare irin wadannan, sai dai ba kasafai kungiyoyin da suke ikirarin jihadi suke daukar alhakin kai wa ba.
Saharar dake Arewacin Nijar tana da girma kuma tana kusa da kasar Libya da masu hada-hadar mutane da kuma ‘yan hijira suke bi suna ratsawa domin shiga cikin kasashen turai.
Kungiyar “Ikilid” wacce ba ta gwamnati ba da take sa ido akan duk wasu rikice-rikice da suke faruwa a duniya, ta ce daga 2023 zuwa yanzu an kashe mutane 2400 a cikin wannan kasa.