Leadership News Hausa:
2025-03-03@16:59:28 GMT

Gwamnatin Kano Za Ta Kashe N2.5bn A Auren Gata

Published: 31st, January 2025 GMT

Gwamnatin Kano Za Ta Kashe N2.5bn A Auren Gata

Bugu da ƙari, Naira miliyan 267.6 an ware su domin shirye-shiryen Addinin Musulunci da tallafa wa waɗanda suka Musulunta, yayin da Naira miliyan 589 za a yi amfani da su wajen bincike kan harkokin tsaro da kuma yaƙi da bara a tituna.

Jimillar kasafin kuɗin Jihar Kano na shekarar 2025 ya kai Naira biliyan 719.

75, wanda ya karu da kashi 31 daga asalin kuɗin da aka gabatar da farko, kuma ya fi na shekarar 2024 da kashi 65.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya

Saɓanin shekarun baya, azumin watan Ramadan na bana ya zo a daidai lokacin da rahotanni ke nuna cewa farashin kayan abinci na sauka a sassan Najeriya.

Kayayyakin masarufi irinsu shinkafa da wake da fulawa na daga cikin waɗanda aka fi sarrafawa a watan na Ramadan, kuma su ne masu gwaggwaɓan kaso a faɗuwar farashin.

Farashin kayan masarufi na sauka a wannan karo ne baya kimanin shekara biyu a jere suna tashi a ƙasar.

Haka kuma, ana iya cewa ’yan Najeriya sun saba ganin tashin farashin kaya, musamman na abinci, a gabnin watan Ramadan.

Duk da mutane suna nuna jin daɗinsu da saukar farashin a wannan karon, amma wasu na cewa hakan bai kawo sauƙi ga talaka ba, a wannan lokaci da aka ɗauki haramar ibadar azumi, saboda rashin kuɗi a hannun jama’a.

An ga watan Ramadan a Najeriya An kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano

Wata matar aure da Aminiya ta zanta da ita ta ce, duk saukar da farashin abinci ke yi, amma ta hatsi ake yi ba ta kayan marmari ba

Ƙarancin masu sayayya

A zagayen da Aminiya ta gudanar a Kasuwar Rimi da ke Kano, ta lura da ƙarancin masu zuwa cefanen azumi a satin jajiberan Ramadan, saɓanin lokutan baya.

Bisa al’ada dai, mata kan yi cefanen kayan abinci na musamman da ake amfani da su a watan azumi, a wasu lokutan ma, har da sabbin mazuban abin ci da sha ga mai gida.

Jiya ta fi yau

Fatima Muhammad Nasir matar aure ce mai ’ya’ya biyu a Kano, ta kuma bayyana wa Aminiya cewa a kowacce shekara idan ta zo gara bara da bana ake a kan farashin kayan abinci a Najeriya.

“A bangarena kayan abincin da suka fi muhimmanci a watan azumi su ne dankali, mai, fulawa, doya, kayan shayi, da aya, zoɓo, wake, gyadar kunu, da sauransu.

Yanzu ta hatsi ake…

“A shekarun baya ina da ƙarfin sayen su nama, kaji, kifi, da doya, da ƙwai amma a bana sai wane da wane.

“Yanzu ta hatsi ake yi ba waɗannan ba. Na baki misali shekaru biyu baya kajin da mai gidan ke saya a kan N7,000 – N11,000 a bana N25,000 zuwa N30,000 ne.

“Gyaɗar kunu a kan N5,000 muka saya kwano ɗaya, aya N1,300, Zoɓo kuma N1,000. Rabin buhun dankali shekaru biyu baya akan N10,000 ne, amma yanzu akan N30,000 ake sayar da shi.”

Ita ma Asma’u Muhammad cewa ta yi tsadar kayan abinci a bana ba kaɗan ba ne idan aka kwatanta da azumin bara.

“Akwai abubuwan da sayen su sai ka ci ka tada kai a yanzu saɓanin baya.

A da, masu girke-girke a soshiyal midiya na yin girkin da muke kallo mu kwaikwaya mu yi a namu gidan, amma yanzu ba komai ne zai yi wu ba.

Ƙalubale

Wata matsala da a azumin bara aka dinga kuka da ita ce ta tsadar ƙanƙara ba da ma ƙarancinta, inda aka dinga sayen manya a kan N500 zuwa sama, ƙanana kuma N300.

Asma’u ta ce babbar matsalar da ke kawo hakan ba ta wuce matsalar rashin wutar lantarki da ta ƙi ci taƙi cinyewa ba, amma a bana tana fatan za a samu sauyi.

“Ƙalubalen da muka fuskanta a bara shi ne tsadar ƙanƙara da rashin wuta. Mutane sun sha wahala saboda an yi rana sosai kuma sanyin da za ka sha an tsuga masa kuɗi. Amma ina fata a bana haka ba za ta faru ba.”

Ita ma Fatima ta bayyana rashin wutar a matsayin babban ƙalubale, musamman a lokutan buɗa baki da sahur.

“Haka muka dinga sahur da buɗa baki a duhu a bara, saboda rashin wuta. Allah Ya sa a bana ba haka za a yi ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar Da Shirin Ciyarwar Na Watan Ramadan
  • An Wallafa Littafin “Zababbun Rubutu Game Da Tattalin Arziki Na Xi Jinping” Kashi Na 1 
  • Ta ina Kungiyar Hizbullah ke samun kuɗaɗenta?
  • Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata A Sani A Kan Kiwon Kifi
  • Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya
  • Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗin 2025 na N54.99trn
  • Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗi na N54.99trn
  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • Wata Mujalla Ta Zabi Shugaban NPA A Matsayin Gwarzonta Na Shekarar 2025