Masu yi wa ƙasa hidima za su karɓi N77,000 daga Fabrairu – Shugaban NYSC
Published: 1st, February 2025 GMT
Shugaban Hukumar yi wa ƙasa hidima ta Najeriya, NYSC Birgediya Janar Yusha’u Dogara Ahmed ya tabbatar wa mambobin shirin da suke aikin yi wa ƙasa hidima na shekara ɗaya cewa za su fara karɓar Naira 77,000 daga watan Fabrairu.
A daidai lokacin da aka sake duba mafi ƙarancin albashi da hauhawar farashin kayayyaki, gwamnatin tarayya ta sanar da ƙarin kuɗaɗen alawus ɗin daga N33,000 zuwa N77,000 duk wata, amma da dama sun nuna damuwarsu kan aiwatar da hakan.
A shekarar bara wani jami’in shirin ya danganta jinkirin aiwatar da biyan kuɗin da rashin kuɗi.
Amma yayin da yake bayani ga mambobin rukunin 2024 Batch ‘C’ Stream II a Jihar Katsina, Ahmed ya tabbatar da cewa an shigar da ƙarin kuɗin a kasafin kuɗin 2025.
Ya ce za a fara aiwatar da shi da zarar an zartar da kasafin kuɗin.
“Tuni gwamnatin tarayya ta amince da ƙarin kuɗaɗen alawus ɗin ku. Ba sabon labari ba ne; abin da muka amince ne da hannunmu. Abin da muke jira shi ne kawai aiwatar da kasafin kuɗin.
“Wannan watan (Janairu) ya riga ya ƙare, amma da zarar an gama kasafin kuɗin, nan da wata mai zuwa (Fabrairu), za ku fara karɓar Naira 77,000 maimakon N33,000 da aka saba karɓa.” In ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Birgediya Janar Yusha u Dogara Ahmed
এছাড়াও পড়ুন:
Sarkin Sasa ya rasu bayan shafe shekaru 125 a doron ƙasa
Allah Ya yi wa Sarkin Sasa, Alhaji Haruna Maiyasin rasuwa bayan shafe shekaru 125 a duniya.
Fadar Sarkin Sasa da ke Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, ce ta bayar da sanarwar rasuwar Sarkin wanda ke riƙe da muƙamin Sardaunan Yamma.
HOTUNA: Gobara ta laƙume shaguna 100 a Kasuwar Sakkwato An raba wa ma’aikatan gona babura 200 a YobeBayanin rasuwar Sarkin Sasa yana ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Ɗan Masanin Sasa, Alhaji Kasim Ado Yaro ya raba wa manema labarai a ranar Asabar.
Ɗan Masanin na Sasa ya ce Alhaji Maiyasin ya rasu ne a yau Asabar bayan fama da rashin lafiya a wani asibiti mai zaman kansa da ke Ibadan.
Sarkin Sasa wanda kuma yake riƙe da muƙamin Shugaban Majalisar Sarakunan Hausawa a jihohi 17 na Kudancin Nijeriya ya rasu ya bar mata 2 da ’ya’ya bakwai.
Sanarwar ta ce za a yi jana’izar Alhaji Haruna Maiyasin a gobe Lahadi.
Aminiya ta ruwaito cewa tun a shekarar 1981 ce aka naɗa Alhaji Haruna Maiyasin a matsayin Sarkin Sasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa wani muhimmin abu da ba za a iya mantawa da shi a tarihin marigayin ba shi ne taimakon bayin Allah da kyautar kuɗi da kayan abinci da suturu bayan aikin jagorancin jama’a da ya sanya a gaba a lokacin yana raye.
Fitowa cikin jama’a ta baya bayan nan da Sarkin Sasa ya yi ita ce lokacin da ya jagoranci manyan Fadawansa zuwa ofishin Gwamnan Jihar Oyo da ke Agodi domin yi wa Gwamna Seyi Makinde ta’aziyar rasuwar yayansa watanni biyu da suka gabata.
Aminiya ta ruwaito cewa yanzu haka Sarakunan Hausawa da Fulani na kusa da birnin Ibadan da manyan malaman Addinin Musulunci suna sun fara zaman makoki a gidan marigayin da ke Sasa zuwa gobe Lahadi da za a yi masa jana’iza.