Aminiya:
2025-04-25@04:58:45 GMT

Masu yi wa ƙasa hidima za su karɓi N77,000 daga Fabrairu – Shugaban NYSC

Published: 1st, February 2025 GMT

Shugaban Hukumar yi wa ƙasa hidima ta Najeriya, NYSC Birgediya Janar Yusha’u Dogara Ahmed ya tabbatar wa mambobin shirin da suke aikin yi wa ƙasa hidima na shekara ɗaya cewa za su fara karɓar Naira 77,000 daga watan Fabrairu.

A daidai lokacin da aka sake duba mafi ƙarancin albashi da hauhawar farashin kayayyaki, gwamnatin tarayya ta sanar da ƙarin kuɗaɗen alawus ɗin daga N33,000 zuwa N77,000 duk wata, amma da dama sun nuna damuwarsu kan aiwatar da hakan.

Gwamna Buni ya zama Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Tafkin Chadi ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 24 a Zamfara

A shekarar bara wani jami’in shirin ya danganta jinkirin aiwatar da biyan kuɗin da rashin kuɗi.

Amma yayin da yake bayani ga mambobin rukunin 2024 Batch ‘C’ Stream II a Jihar Katsina, Ahmed ya tabbatar da cewa an shigar da ƙarin kuɗin a kasafin kuɗin 2025.

Ya ce za a fara aiwatar da shi da zarar an zartar da kasafin kuɗin.

“Tuni gwamnatin tarayya ta amince da ƙarin kuɗaɗen alawus ɗin ku. Ba sabon labari ba ne; abin da muka amince ne da hannunmu. Abin da muke jira shi ne kawai aiwatar da kasafin kuɗin.

“Wannan watan (Janairu) ya riga ya ƙare, amma da zarar an gama kasafin kuɗin, nan da wata mai zuwa (Fabrairu), za ku fara karɓar Naira 77,000 maimakon N33,000 da aka saba karɓa.” In ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Birgediya Janar Yusha u Dogara Ahmed

এছাড়াও পড়ুন:

Mutanen da aka kashe a Binuwai sun ƙaru zuwa 72

Adadin mutanen da suka mutu a hare-haren da aka kai a Jihar Binuwai ya ƙaru zuwa 72.

Adadin ya ƙaru ne bayan gano ƙarin gawarwaki 13 a ranar Litinin a ƙananan hukumomin  Ukum da Logo.Adadin ya ƙaru ne bayan gano ƙarin gawarwaki 13 a ranar Litinin a ƙananan hukumomin  Ukum da Logo.

Da farko a ranar Lahadi Gwamna Hyacinth Alia a yayin da yake jawabin Ista a wani coci, ya sanar a yayin cewa an gano gawarwaki 59.

Daga bisani aka gano ƙarin gawarwaki a cikin jejin yankunan da aka kai hare-haren.

Kakakin gwmanan jihar, Isaac Uzaan, ya bayyana cewa an gano ƙarin gawarwaki 12 a Ƙaramar Hukumar Uku sauran mutum ɗaya kuma a Logo.

Tsakanin daren ranar Alhamis da safiyar Juma’a ne kai hare-hare a ƙauyukan yankin Sankera wanda ya ƙunshi ƙananan hukumar Ukum, Logo, and Kastina-Ala.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta amince ta bai wa mahajjata kuɗin guzirinsu a hannu
  • Kasar Yemen Zata Aiwatar Da Abubuwan Mamaki Da Zasu Firgita Makiyanta Kuma Abokan Gaba
  • Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe
  • Tinubu ya gana da shugabannin tsaro a Abuja
  • CONMEBOL ta buƙaci a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta 2030
  • Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka
  • 2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
  • Mutanen da aka kashe a Binuwai sun ƙaru zuwa 72
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Boko Haram A Yobe
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Kundin Tsarin Mulkin Najeriya?