Sin Ta Mayar Da Martani Ga Shirin Japan Na Aiwatar Da Matakan Hana Fitar Da Kayayyaki Zuwa Sin
Published: 1st, February 2025 GMT
Yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar kasuwanci ta Sin ya amsa tambayoyin ‘yan jarida game da shirin Japan na aiwatar da matakan hana fitar da kayayyaki zuwa Sin, ciki har da semiconductor.
Kakakin ya bayyana cewa, shirin bangaren Japan na aiwatar da matakan, zai kawo cikas ga tsaro da kwanciyar hankali na tsarin masana’antu, da gurgunta mu’amalar kasuwanci na yau da kullum dake tsakanin kamfanoni, da kuma lalata muradun kamfanonin kasashen biyu.
Sin na fatan kasar Japan za ta ji ra’ayoyin masana’antu, ta kuma gaggauta gyara ayyukan da ta yi bisa tushen kiyaye ka’idojin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa, da moriyar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da Sin.
Bugu da kari, ya ce kasar Sin za ta dauki matakan kiyaye hakki da moriyarta.(Safiyah Ma)
এছাড়াও পড়ুন:
CBN Ya Umarci Daraktocin Bankuna Su Mayar Da Bashin Da Suka Karba Ko Su Yi Murabus
Bankin na CBN ya sanar da cewa, daukacin Bankunan, ana sa ran su bi wannan umarnin nan take.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp