HausaTv:
2025-03-03@18:22:02 GMT

Hizbullah Ta Yi Alhinin Sahadar Muhammad Dhaif Kwamandan Rundunar Kassam Ta Hamas

Published: 1st, February 2025 GMT

A wani bayani da kungiyar ta Hizbullah ta fitar ta bayyana alhininta na shahadar babban hafsan mayakan rundunar “Kassam” ta kungiyar Hamas Muhammad Dhaif  tare da wasu abokan aikinsa, tare da bayyana rawar da  suka taka a fagen gwagwarmaya.

Kungiyar ta Hizbullaha ta mika sakon ta’aziyya da kuma barka akan shhadar Muhammad Dhaif ga kungiyar gwgawarmayar musulunci ta Hamas da sauran kungiyoyin Falasdinawa da kuma al’ummar Falasdinu.

Haka nan kuma kungiyar ta Hizbullah ta mika sakon ta’aziyyar ga iyalan shahidan.

Kungiyar gwgawarmayar musuluncin ta Lebanon ta kuma ambaci cewa, Muhammad Dhaif ya tafiyar da dukkanin rayuwarsa ne wajen fada da ‘yan sahayoniya da kwankwasar kansu, musamman ma dai a yayin farmakin Aksa, da ya kasance daya daga cikin fitattun wadanda su ka shriya shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida

Rahotanni da suke fitowa daga Nijar sun bayyana cewa; Wata kungiyar mai alaka da al-ka’ida ta  dauki alhakin kashe sojojin kasar 11 a kan iyaka da Aljeriya.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne dai lamarin ya faru,kuma a jiya Asabar ne aka yi jana’izarsu a garin Agadez, kamar yadda wata majiyar watsa labara ta jamhuriyar Nijar ta ambata.

Shafin “Air Info” da ya watsa laabrin ya kuma ce; Jami’an soja da dama sun hjalarci jana’izar sojojin da su ka kwanta dama, daga cikinsu har da janar Musa Salih Barmo, babban hafsan hafsoshin sojan kasar.

Tashar Radiyo din kasar ta Nijar ta ce, an yi wa sojojin kwanton bauna ne a lokacin da suke sintiri akan  mahadar iyakaokin kasar, da Mali da kuma Burkina Faso.

Labarin Radiyon ya kuma ce, Janar Barmo ya nufi asibitin garin Agadez din domin yin dubiyar sojojin da su ka jikkata.”

 A gefe daya wata kungiyar mai  suna; “Nasratul-Islam Wal Muslimin” da reshe ne na alka’ida, ta dauki alhakin kai harin.

A lokuta da dama a baya sojojin na jamhuriyar Nijar sun sha fuskantar hare-hare irin wadannan, sai dai ba kasafai kungiyoyin da suke ikirarin jihadi suke daukar alhakin kai wa ba.

Saharar dake Arewacin Nijar tana da girma kuma tana kusa da kasar Libya da masu hada-hadar mutane da kuma  ‘yan hijira suke bi suna ratsawa domin shiga cikin kasashen turai.

Kungiyar “Ikilid” wacce ba ta gwamnati ba da take sa ido akan duk wasu rikice-rikice da suke faruwa a duniya, ta ce daga 2023 zuwa yanzu an kashe mutane 2400 a cikin wannan kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar ECOWAS Ta Fice Daga Guinea-Bissau Bayan Barazana Daga Shugaban Kasar
  • Hamas: Babu Wani Karin Tattaunawa Da HKI, A Aiwatar Da Yarjeniyar Kamar Yadda Take
  • Ɓacewar bindigogi 4,000: Sakaci ne dalili —’Yan sanda
  • Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida
  •  Hamas: Matakin Netenyahu Na Dakatar Da Shigar Kayan Agaji Cikin Gaza Keta Yarjejeniya Ne
  • Ta ina Kungiyar Hizbullah ke samun kuɗaɗenta?
  • Shin Liverpool Za Ta Kai Labari Ba Tare Da Muhammad Salah Ba?
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Masallacin Juma’a A Garin Samamiya Da Ke Birnin Kudu
  • Hukumar Lamuni Ta Duniya IMF Da Bankin Duniya Sun Ce Bazasu Taimakawa Lebanon Ba Sai Da Sharudda
  • An Yi Jana’izar Shahidan kungiyar Hizbullah Fiye Da 120 Kudancin Kasar Lebanon A Yau Jumma’a