Hajjatul-Islam Wal Muslimin Muhammad Hassan Abu Turabi da ya jagoranci Sallar juma’a a Tehran a jiya juma’a ya bayyana Imam Khumaini ( r.a) a mastayin daya daga cikin fitattun mutanen da duniyar musulunci ta samu a wannan zamanin.

Hujjatul-Islam Wal Muslimin ya ce, Shakshiyya din Imam Khumaini ta ginu ne akan ilimomi na addini,filiku da falsafa.

Limamin juma’ar na Tehran wanda yake jawabi dangane da zagayowar cikar shekaru 46 daga dawowar Imam Khumaini Iran bayan zaman hijira na shekaru 15 a kasashen waje, ya ce abin alfahari ne yadda wannan rana ta zagayo a daidai wannan lokacin da kungiyoyin gwgagwarmayar musulunci suke kara bunkasa da daukaka a duniyar musulunci.

Hujjatul-Islam Wal Muslimin Abu Turabi ya kuma bayyana cewa abinda yake da muhimmanci a wannan lokacin shi ne ci gaba da aiki akan tafarkin Imam Khumaini cikin tsayuwar daka ba tare da girgiza ba.

Limamin juma’ar na Tehran ya ce kamar yadda abokan gabarmu suke jurewa wajen fuskantarmu, to mu ma ya zama wajibi a gare mu da mu yi tsayin daka wajen fuskantarsu, tare da yin ishara da abinda ya faru a Gaza, da kuma kallafaffen yaki akan Iran yana mai kara da cewa; Ba domin gwagwarmaya ba ta al’ummar Iran da su ka hada da dakarun kare juyin musulunci da sojoji a wancan lokacin, to da abubuwan da suke faruwa na alfahari ga al’ummar Musulmi a wannan lokacin ba su faru ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Neman Yin Lalata: Ina Da Kwararan Hujjoji Akan Akpabio – Natasha 

Sai dai, a martanin da ta yi ta bakin lauyanta a ranar Asabar, Giwa ya bukace matar Sanata Akpabio ta da janye kanta a rikicin don bai wa mijinta damar kare kansa saboda wanda yake karewa tana da “kwakkwarar hujja da za ta tabbatar da zarginta.”

 

Sanata Natasha ta kai karar Akpabio da mai taimaka masa, Mfon Patrick gaban kotu, inda ta bukaci diyyar Naira Biliyan 100.3 bisa zargin bata mata suna bayan takaddamar da ta biyo bayan sauya mata kujera a zauren majalisar dattawa.

 

Sanata mai wakiltar Kogi ta Arewa, wacce aka dakatar kuma aka mika wa kwamitin da’a na majalisar dattawa koke akanta, a yayin wata hira da gidan talabijin, ta ce, Sanata Akpabio ya ki amincewa da bukatarta kan yanayin kamfanin karafa na Ajaokuta saboda ta ki amincewa da buƙatar shi na neman yin lalata da ita.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa Sirar Imam Alhassan(99)
  • Masana Fasahar Gina Jiragen Sama A Iran Sun Samar Da Wata Fasahar Nano Mai Rage Nauyin Jiragen Sama
  • Jagora: Iran Tana Fuskantar  Makiya Na Waje Kafirar Da Munafikai
  • Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha
  • Zargin Neman Yin Lalata: Ina Da Kwararan Hujjoji Akan Akpabio – Natasha 
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Masana’antar Kannywood: Da Tsohuwar Zuma… -Fassarar Farfesa Uba Adamu
  • Iran Ta Zama Zakara A Damben Gargajiya Ta 2025 UWW Wanda Aka Gudanar A Kasar Albaniya
  • Habasha Da Somaliya Sun Tattaunawa Hanyoyin Sake Mayar Da Alaka
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Masallacin Juma’a A Garin Samamiya Da Ke Birnin Kudu