Hajjatul-Islam Wal Muslimin Muhammad Hassan Abu Turabi da ya jagoranci Sallar juma’a a Tehran a jiya juma’a ya bayyana Imam Khumaini ( r.a) a mastayin daya daga cikin fitattun mutanen da duniyar musulunci ta samu a wannan zamanin.

Hujjatul-Islam Wal Muslimin ya ce, Shakshiyya din Imam Khumaini ta ginu ne akan ilimomi na addini,filiku da falsafa.

Limamin juma’ar na Tehran wanda yake jawabi dangane da zagayowar cikar shekaru 46 daga dawowar Imam Khumaini Iran bayan zaman hijira na shekaru 15 a kasashen waje, ya ce abin alfahari ne yadda wannan rana ta zagayo a daidai wannan lokacin da kungiyoyin gwgagwarmayar musulunci suke kara bunkasa da daukaka a duniyar musulunci.

Hujjatul-Islam Wal Muslimin Abu Turabi ya kuma bayyana cewa abinda yake da muhimmanci a wannan lokacin shi ne ci gaba da aiki akan tafarkin Imam Khumaini cikin tsayuwar daka ba tare da girgiza ba.

Limamin juma’ar na Tehran ya ce kamar yadda abokan gabarmu suke jurewa wajen fuskantarmu, to mu ma ya zama wajibi a gare mu da mu yi tsayin daka wajen fuskantarsu, tare da yin ishara da abinda ya faru a Gaza, da kuma kallafaffen yaki akan Iran yana mai kara da cewa; Ba domin gwagwarmaya ba ta al’ummar Iran da su ka hada da dakarun kare juyin musulunci da sojoji a wancan lokacin, to da abubuwan da suke faruwa na alfahari ga al’ummar Musulmi a wannan lokacin ba su faru ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Kebance Jiragen Saman Yaki Na Kai Hari Kan ‘Yan Sahayoniyya

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta Sanar da cewa: Ma’aikatar tsaron kasar ta kebe jirgin saman maras matuki ciki kirar “Arash-2” da ta kera ne don kai hari kan haramtacciyar kasar Isra’ila

A ci gaba da gudanar ranakun atisayen soji domin ayyukan tsaron kasa, da sojojin Iran suke gwajin kai hare-hare da kuma sarrafa manyan na’urorin makaman tsaro a yankin da ke yammacin kasar, a karon farko sun nuna wasu jiragen saman yaki maras matuki ciki da aka kera a cikin gida masu tsnanin karfin munanan hare-hare irin na kunan bakin wake kirar “Ababil” da “Arash-2” da dakarun sojin kasar Iran zasu yi amfani da su wajen kare tsaron kasa duk lokacin da ya dace.

Jiragen saman “Ababil” ne suka jagoranci tawagar sabbin makaman, sannan wasu jiragen saman kunar bakin wake guda uku na “Arash” suka biyo bayansu, wadanda idan aka kai hari da su zasu tarwatsa wuraren da aka tura su.

Abin lura shi ne cewa: “jirgin Arash-2 yana ci nisan kilomita 2,000, wanda ya sa ya zama jagora a tsakanin takwarorinsa na jiragen saman yakin Iran da ma duniya baki daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisoshin Rayuwa: Imam AlHassan (a)
  • Kissoshin Rayuwa Imam Hassan (a) 09
  • An Fara Bukukuwan Kwanaki Goma Na Cin Nasarar Juyin Juya Halin Musulinci A Iran   
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Bukatar Bunkasa Alakarta Da Kasar Qatar
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Kebance Jiragen Saman Yaki Na Kai Hari Kan ‘Yan Sahayoniyya
  • Kungiyar Hams Ta Jinjinawa Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Goyon Bayan Gwagwarmaya
  • JMI Ta Cika Shekaru 46 Cib Da Nasarrar Juyin Juya Halin Mususlunci A Kasar, Wani Irin Ci gaba Ne Ta Samu A Cikin Wannan Lokacin
  • NAJERIYA A YAU: Ainihin Dalilan Taƙaddama Kan Kafa Kotunan Musulunci A Kudu
  • Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici