HausaTv:
2025-02-01@08:40:10 GMT

 Fizishkiyan: Gwagwarmaya Za Ta Yi Karfin Da Ba Za Iya Rusa Ta Da Makamai Ba

Published: 1st, February 2025 GMT

Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana cewa; babbar matsalar da  duniyar musulmi ke fuskanta ta samo tushe ne daga yin isa daga koyarwar musuluncin, da babu abinda hakan ya haddasa sai rabuwar kawuna da sabani, ya kuma bai wa makiya kafar da za su shiga.

Shugaban kasar ta Iran wanda ya aike da sako zuwa wurin rufe ‘gasar karatun akur’ani mai girma karo na 41 da aka yi a birnin Mashhad, ya bayyana cewa; Alkur’ani mai girma yana yin Magana ne da musulmi a matsayin al’umma daya dunkulalliya, yake kuma yin kira a gare su da su yi riko da igiyar Allah da hadinkai, domin hana rabuwar kawuna.

Shugaban na kasar Iran ya kuma ce; Shakka babu, wani sashe mai girma na matsalolin da duniyar musulmi take fuskanta a wannan lokacin sakamako ne na nesantar koyarwar al’kur’ani, wanda kuma babu abinda hakan yake haifarwa sai rabuwar kawuna da kuma bude kafa a gaban makiya ‘yan adamtaka.”

Shugaba Fizishkiyan ya kuma ce; shi alkur’ani mai girma yana yin Magana ne da dukkanin bil’adama ba tare da la’akari da launinsu ko ajinsu ba, ko kuma addinin da suke yi,kuma ya nuna wa jinsin dan’adam hanyar kai wa ga kamala.

Haka nan kuma shugaban na kasar Iran ya ce, a karkashin koyarwar addinin musulunci, mutane za su sami madogara mai karfi mai nagarta a cikin wannan duniyar da take cike da rudani.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Hare Kan Fararen Hula A Rikicin Da Ake Yi A Kasar Sudan

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi Allah wadai da harin da aka kai kan fararen hula a Sudan

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi Allah wadai da kisan fararen hula a hare-haren da ake kai wa kan asibitoci da cibiyoyin jama’a a Sudan tare da jaddada wajibcin mutunta ka’idoji da dokokin kare hakkin bil’adama a kasar.

Baqa’i” ya yi Allah wadai da kisan mutane a hare-haren da ake kai wa kan fararen hula da ababen more rayuwa, musamman asibitoci da cibiyoyin jama’a a Sudan.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya bayyana juyayinsa ga wadanda harin baya-bayan nan ya rutsa da su, musamman a birnin El Fasher fadar mulkin Darfur ta Arewa, inda ya jaddada bukatar kiyaye ka’idoji da na dokokin jin kai na kasa da kasa, musamman ka’idar haramta kai hare-hare kan wuraren fararen hula, tare da yin kira da a kawo karshen tashe-tashen hankula da samar da hanyoyin warware rikicin da ke faruwa a Sudan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Ranar Basirah: 9TH Day A Wajen JMI
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Bukatar Bunkasa Alakarta Da Kasar Qatar
  • Kungiyar Hams Ta Jinjinawa Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Goyon Bayan Gwagwarmaya
  • Cece-kuce Ya Barke Kan Shirin “Kur’anic Convention”
  • Natanyahu Ya Bada Umurnin A Dakatar Da Musayar Fursinoni Da Kungiyoyi Masu Gwagwarmaya A Gaza
  • Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamna Lawal ya Yaba Wa DSS Kan Bankaɗo Makamai A Jihar Zamfara 
  • Nukiliya : Babu Wani ‘Musayar Sako’ Tsakaninmu Da Amurka_ Araghchi  
  • Sojoji Sun Ƙwato Makamai, Sun Ci Gaba Da Neman Bello Turji A Zamfara
  • Kasar Iran Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Hare Kan Fararen Hula A Rikicin Da Ake Yi A Kasar Sudan