HausaTv:
2025-04-23@01:37:38 GMT

DRC: ‘Yan Tawayen M 23 Sun Sha Alwashin Tunkarar Babban Birnin Kasar Kinshasha

Published: 1st, February 2025 GMT

Bayan da su ka kwace iko da birnin Goma dke gabashin kasar DRC, kungiyar ‘yan tawaye ta M 23 wacce take samun goyon bayan kasar Rwanda ta sha alwashin kama hanyar shiga  babban birnin kasar Kinsasha.

Wani daga shugabannin kungiyar ta M 23, Corneilla Nangaa ya furta cewa,: manufarmu  ita ce, muna yin yaki ne saboda kishin Congo, ba muna yaki ne saboda samun ma’adanai ba, babu wani dalili na daban da ya sa muke yaki.

Da akwai wasu rahotanni da suke nuni da cewa, ‘yan tawayen na M 23 sun kama hanyar zuwa Bukavu, wanda shi ne birni mafi girma na biyu a yankin.

Nangaa ya ce babu wata gwamnati tsayayya a kasar Congo, domin Tshikedi ya riga ya rusa sojoji, ‘yansanda, kuma tsarin tafiyar da mulki, haka nan kuma ma’aikatar shari’a.”

Sai dai kuma ‘yan  tawayen sun ce a shriye suke a bude tattaunawa domin a dama da su a cikin sha’anin tafiyar da kasar.

Kungiyoyin kasa da kasa suna yin kira da a tsagaita wutar yaki a kasar ta DRC.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Lebanon Sun Kama Wasu Mutanen Da Suke Shirin Cilla Makamai Kan HKI

Majiyar labarai daga kasar Lebanon sun bada sanarwa kama wasu mutane wadanda suke shirin Cilla Makamai kan HKI.

Jaridar Arab News ta yanar gizo ta kuma kasar Saudiya ta bayyana cewa a makon da ya gabata ma an kama wasu mutane wadanda ake zargi da cilla makaman roka kan HKI daga kudancin kasar ta Lebanon.

Amma dangane da kwance damarar kungiyar Hizbullah kuma shugaban kasar Lebanon Jesept Aun ya ce wannan al-amarin ba abu ne mai sauki ba, sai dai a jira lokacinda ya dace na yin hakan. Aun ya kara da cewa duk wani kokari na kwance damarar kungiyar hizbullah kawo karshen zaman lafiya a kasar Lebanon ne.

Kafin haka dai shugaban kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kasim a jawabin da ya gabatar a ranar Jumma’a ya bayyana cewa ba wanda ya ida ya kwace, makaman kungiyar amma kungiyar zata iya tattainawa don kyautata tsaron kasar Lebanon tare da sauran jami’an tsaron kasar.

Wasu masana suna ganin da alamun wasu jami’an gwamnatin kasar Lebanon sun zama wakilan HKI da Amurka a kasar. Musamman ganin yadda HKI ta kai hare-hare har sau 2700 bayan tsagaita bude wuta da kungiyar Hizbulla, ba zakat aba jin wani yayi magana a kansa ba, amma suna maganar kwance damarar kungiyar ta Hizbullah.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna
  • An sanya dokar hana fita ta sa’o’i 12 a Neja
  • Darajar Cinikin Sarin Kaya Da Sayen Kayan Masarufin Sin Ta Karu Da Dala Biliyan 452.5 a Rubu’In Farkon Bana
  • Shugaban Ma’aikatar Shari’a Yana Halartar Taro A Kasar China
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • Idan Shugaban Kasar Siriya Mai Ci Ya Taka Kasar Iraki Ana Iya Kama Shi
  • Sojojin Lebanon Sun Kama Wasu Mutanen Da Suke Shirin Cilla Makamai Kan HKI
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Bada Tallafin Kudi Ga Manoman Alkama
  • Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma