Kashi 85 Na Inibin Da Ake Nomawa Nijeriya, Daga Jihar Kaduna Ne – Dalhatu
Published: 1st, February 2025 GMT
Shugaban ya kara da cewa, a shekarar farko ne ake fara girbe reshensa, sannan kuma bishiyar tasa na daukar tsawon shekara 50 ana amfana da ita.
“A shekara, sau biyu ake girbe Inibi, sannan idan aka ajiye ganyensa a kan tebur, yana shafe daga kwana 45 zuwa 50 ba tare da ya lalace ba”, in ji shi.
Ya ci gaba da cewa, Allah ya albarkaci Arewacin Nijeriya da kasar nomad a kuma yanayi mai kyau, musamman ma Karamar Hukumar Kudan ta Jihar Kaduna, inda ake iya shuka wannan Iri na Inibi, ya girma; a kuma amfana da shi.
Shugaban ya sanar da cewa, kimanin kashi 85 cikin 100 na Inibin da ake nomawa a kasar nan, na fitowa ne daga Karamar Hukumar Kudan.
Shi kuwa, Shugaban Karamar Hukumar ta Kudan; Dauda Iliya Abba, yaba wa manoman ya yi, kan mayar da hankalin da suke yi a yayin noman nasu Inibi, inda kuma ya jaddada kudirin Gwamnan Jihar, Sanata Uba Sani, na ci gaba da bai wa fannin aikin noma goyon bayan da ya dace.
এছাড়াও পড়ুন:
Ramadan: Coci ya ciyar da Musulmi 1,000 a Kaduna
Cocin Christ Evangelical & Life Intercessory Ministry da ke yankin Sabon Tasha a Ƙaramar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, ya raba wa makarantun Islamiyya Musulmi masu ƙaramin ƙarfi akalla 1,000 hatsi albarkacin watan Ramadan.
Shugaban Cocin, Fasto Yohanna Buru, ya ce sun yi haka ne domin yauƙaƙa dangantaka da kuma wanzar da zaman lafiya a tsakanin Musulmi da makwabtansu mabiya wasu addinai a yankin.
Ya ce, “muna mayar da biki ne bisa alherin da Hajiya Ramatu Tijjani, wadda ta tsaya kai da fata wajen rabon shinkafa, kuɗi, da tufafi ga marayu da zawarwan cocinmu a lokacin Kirsimeti da Sabuwar Shekara da kuma Ista.”
Fasto Buru, ya ce cocin janyo irin wannan rabon abinci ga Musulmi a jihohi biyar a tsawon shekaru 19, domin sama musu sauƙi a watan Ramadan.
Ɓacewar bindigogi 4,000: Sakaci ne dalili —’Yan sanda Yadda ’yan bindiga suka sace ɗalibai 4 a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma“Bana mun tsara tallafa wa Musulmi 1,000 kuma mun riga mun tanadi buhunan hatsi domin raba musu,” in ji shi.
Ya buƙaci masu hannu da shuni su taimaka wa mabuƙata, tare da roƙon ’yan kasuwa da su guji tsawwala farashin kayan masarufi a watan Ramadan.
Ya ce fastoci da limamai kimanin 30 sun sadaukar da kansu domin gudanar da gangamin kiran ’yan kasuwa su daina ƙara farashin kayan masarufi a watan Ramadan.