Aminiya:
2025-04-02@20:54:08 GMT

Yadda Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass ya yi wa Tinubu addu’ar nasara

Published: 1st, February 2025 GMT

Shugabannin Ɗariƙar Tijjaniyya bisa jagorancin Khalifa Sheikh Muhammad Mahi Inyass, sun ziyarci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadarsa.

A yayin ziyarar, Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass kuma ɗansa, Khalifa Sheikh Muhammad Mahi, da tawagarsa sun halarci Sallar Juma’a tare da Shugaba Tinubu a Fadar Shugaban Ƙasa.

Malaman sun kuma gudanar da addu’o’in neman taimakon Allah da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci-gaba da kuma albarka ga Najeriya.

Khalifa Muhammad Mahi Inyass, ɗa ga Jagoran Tijjaniyya Sheikh Ibrahim Inyass, ya jinjina wa Gwamnatin Tinubu, inda ya yi wa shugaban ƙasa addu’ar samun nasara da ƙarin basira da nasara a shugabanci domin kawo gagarumar ci-gaba a Najeriya.

Masu yi wa ƙasa hidima za su karɓi N77,000 daga Fabrairu – Shugaban NYSC ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 24 a Zamfara

Khalifa Mahi Inyass ya shaida wa manema labarai cewa tawagar ta taso ne musamman daga ƙasar Senegal, mahaifar Sheikh Ibrahim Inyass, domin halartar Maulidin Tijjaniyya na Sheikh Inyass na wannan shekara.

Ya ba wa Shugaba Tinubu tabbacin goyon baya da addu’o’i musamman daga mabiya ɗarikar Tijjaniyya sam da miliyan 400 da ke Najeriya da sauran wurare.

’Yan tawagar sun haɗa da Sheikh Ibrahim, babban ɗan Sheikh Dahiru Usman Bauchi, da dai sauran shugabannin Ɗariƙar Tijjaniyya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Darikar Tijjaniyya Inyass Mahi Ibrahim Inyass Tijjaniyya Sheikh Ibrahim Inyass

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi

Shugaba Tinubu, a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ya fitar, ya bayyana marigayin a matsayin babban ginshikin masarauta kuma mai neman ci gabanta.

 

Shugaba Tinubu ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Kano da majalisar masarautar Kano da kuma iyalan marigayin bisa wannan rashi mara misaltuwa.

 

Shugaban ya yi addu’ar Allah ya sa Jannatul Firdaus, ta zama makoma ga Galadima.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi
  • Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi
  • Tinubu Ya Tafi Faransa Ziyarar Aiki Na Mako 2
  • Tinubu zai tafi ziyarar makonni biyu a Faransa
  • Shugaban Tinubu Ya Tube Kyara A Matsayin Shugaban Kamfanin NNPC Ya Kuma Sannan Ya Maye Gurbinsa
  • Tinubu ya cire Mele Kyari daga shugabancin NNPC
  • DG VON Yayi Kira Ga Zaman Lafiya Da Hadin Kai Don Fadada Ci gaban Tattalin Arziki Da Ci Gaba.
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Za Su Kwaɗaita Muku Azumtar Sitta Shawwal
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
  • Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama