Gwamna Radda Ya Samar Da Keke Napep Don Saukaka Zirga-zirga A Katsina
Published: 1st, February 2025 GMT
Shi ma da yake jawabi, shugaban kungiyar masu tuka ‘yar kurkurar, Jamilu Isyaku ya bayyana jin dadinsa ga Gwamna Radda bisa amsa kiran da suka yi masa na biya masu bukatunsu kan sama masu da keke napep mai amfani da lantarki da kuma ba da tabbacin yin amfani da su yadda ya kamata.
.এছাড়াও পড়ুন:
Babu Wata Suka Da Za Ta Hana Gwamna Dauda Lawal Aiwatar da Ayyuka.
Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewa babu wani kamfen batanci da zai hana Gwamna Dauda Lawal aiwatar da ayyukan da suka shafi al’umma a fadin jihar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labarai da sadarwa na gwamna, Malam Salihu Nuhu Anka ya rabawa manema labarai a Gusau.
A cewar Anka, Gwamna Lawal ya fara aiki ne a wani aikin ceto, kuma tuni mazauna jihar suka fara cin ribar dimokuradiyya.
Ya bayyana cewa hankalinsa ya karkata ne kan kalaman da ya bayyana a matsayin maras tushe da wani tsohon Kwamishinan Yada Labarai, Ibrahim Magaji Dosara ya yi, yayin wani taron manema labarai a Kaduna, inda ya kalubalanci kalaman da Gwamna Lawal ya yi a wata hira da ya yi da shi kwanan nan.
“A yayin taron manema labarai, Dosara ya kai wa Gwamna Dauda Lawal hari cikin rashin kunya a kokarinsa na burge tsohon Gwamna Bello Matawalle,” Anka ya yi zargin.
REL/AMINU DALHATU.