Karfin Diblomasiyyar Kasar Iran Ce Ya Sa Ta Bayyana Karfin Kayakin Yakinta Wa kasashen Yankin
Published: 1st, February 2025 GMT
Sojojin kasar Iran sun nuna karfinsu a yankin Asiya ta kudu tare da itisayen da ta yi ta gudanarwa a cikin yan makonnin da suka gabata. Tare da nuna iya diblomasiyyar kasar tare da sauran kasashen yankin.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Rear Admiral Habibollah Sayyari mataimakin shugaban rundunar sojiji na kasar yana fadar haka.
Kuma ta tabbatar da cewa zata iya kula da al-amuran tsarom da kuma tabbata shi a yankin. Sayyari yace an gudanar da atisayen na sojoji kimani rundunonin fiya da 100 inda suka yi musayar tunani da dabar barun yaki a tsakaninsu, inda da dama daga cikinsu sojojin kasashen waje ne.
Yace a cikin wadannan atisai daban-daban sun yi amfani da sabbin makamai da kasar ta kera da kuma sabbin dabarbarun yaki. Daga karshe Sayyari ya bayyana cewa mai suna ‘Zulfikar’ sojojin kasar Iran zasu nuna karfinsu a fagen kayakin aikin zamani da kuma sabbin dabarbarun yaki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kotun Kasa Da Kasa Zata Fitar Da Sammacin kama Masu Hannu A Aikata Muggan Laifuka A Darfur Na Sudan
Kotun da ke shari’ar manyan laifuka a duniya tana gab da fitar da sammacin neman kama wadanda suka aikata muggan laifukan Darfur na kasar Sudan
Mai gabatar da kara na kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, Karim Khan, ya sanar da cewa ofishinsa zai bukaci fitar da sammacin kama wadanda ake zargi da aikata ta’asa a yankin yammacin Darfur na kasar Sudan nan kusa kadan.
Karim Khan ya bayyana wa Kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya cewa: Ana aikata muggan laifuka a yankin Darfur da ke yammacin kasar Sudan a lokacin da muke magana kan halin yankin da kuma kullum rana a matsayin makamin yaki a kasar.
Khan ya kara da cewa hakan ya samo asali ne sakamakon bincike da aka gudanar a tsanake bisa hujjoji da bayanan da ofishinsa ya tattara.