Sojojin kasar Iran sun nuna karfinsu a yankin Asiya ta kudu tare da itisayen da ta yi ta gudanarwa a cikin yan makonnin da suka gabata. Tare da nuna iya diblomasiyyar kasar tare da sauran kasashen yankin.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Rear Admiral Habibollah Sayyari mataimakin shugaban rundunar sojiji na kasar yana fadar haka.

Ya kuma kara da cewa, iya diblomasiyyar kasar Iran a tsakanin  kasashen yankin, ya tabbatar da karfin da kasar take da shi a fagen karfin soje.

Kuma ta tabbatar da cewa zata iya kula da al-amuran tsarom da kuma tabbata shi a yankin. Sayyari yace an gudanar da atisayen na sojoji kimani rundunonin fiya da 100 inda suka yi musayar tunani da dabar barun yaki a tsakaninsu, inda da dama daga cikinsu sojojin kasashen waje ne.

Yace a cikin wadannan atisai daban-daban sun yi amfani da sabbin makamai da kasar ta kera da kuma sabbin dabarbarun yaki. Daga karshe Sayyari ya bayyana cewa mai suna ‘Zulfikar’ sojojin kasar Iran zasu nuna karfinsu a fagen kayakin aikin zamani da kuma sabbin dabarbarun yaki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yemen Ta Ce A Shirye Take Ta Koma Yaki Idan Yaki Ya Sake Barkewa A Gaza

Shugaban kungiyar Ansarullah Sayyid Abdulmalik Badruddeen Huthi ya bayyana cewa kasar Yemen a shirye take ta sake shiga yaki idan yarjeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu ta wargaje.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Sayyid Huthi yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar ta hotunan bidiyo a jiya 28 ga watan Fabrairun shekara ta 2025.

Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya bayyana cewa birnin Tel’aviv wato Yafa, zai zama babban wurin da makaman kungiyar zasu nufi idan hakan ya faru.

Huthi ya ce “Idan yaki ya sake barkewa za mu kai hare-hare a ko ina a HKI sannan birnin Tel’aviv zai za ma babbar manufar makamammu.

Yace: Kasar Yemen ta na kallom yadda al-amura suke tafiya a ayyukan tsagaita wutar, kuma ta na kallon yadda HKI take sabawa wasu abubuwan da ke cikin yarjeniyar. Ya kuma ambaci yadda HKI ta ki janyewa daga rafah da kuma yankin philidelfiya na kan iyaka da kasar Masar. Wanda kuma ya sabawa yarjeniyar. Sannan ya kammala da cewa gwamnatin kasar Amurka ta na kodaitar da HKI da yin hakan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya
  • Masar Za Ta Bayyana Shirin Sake Gina Gaza A Yayin Taron Larabawa
  • Junbilat: ‘Yan Sahyoniya Suna Son Tarwatsa Kasar Syria
  • Kasashen Somaliya Da Habasha Suna Gab Da Rattaba Hannu Akan Amfani Da Tashar Jirgin Ruwa
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Motocin Buldoza Suna Ta Rusa Gidajen Falasdinawa A Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Sin Ta Kiyaye Girmama Kasashen Tsibirai Na Yankin Tekun Pasifik
  • Yemen Ta Ce A Shirye Take Ta Koma Yaki Idan Yaki Ya Sake Barkewa A Gaza
  • Habasha Da Somaliya Sun Tattaunawa Hanyoyin Sake Mayar Da Alaka