Shugaban kasar Iran Ma’suod Pezeskiyan tare da majalisar ministocinsa sun sabonda bai’a da jagoran juyin juya halin musulunci, wanda ya kai kasar ga samun nasarar tumbuke gwamnatin sarki Muhamma Reza Sha sannan ya sannan ya kaisu ga nasarar kafa JM a Iran,  shekaru 46 da suka gabata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa a safiyar yau Asabar ce shugaban kasar Iran, Masuod Pezeshikyan tare da majalisar ministocinsa suka kara sabonta bai’a wato marigayi Immam Khomani (q).

 

Labarin ya kara da cewa Sayyid Hassan Khomani, jikan Imam(q) wanda kuma yake kula da hubbaren nasa ne, ya tarbi shugaban kasar ya kuma jagorance su zuwa hubbaren kakansa Imam Khumaini(q).

Imam Khomani (q) ne ya jagoranci mutanen kasar Iran zuwa kifar da gwamnatin sarki sha, shekaru 46 da suka gabata, a ranar 11 ga watan Fabrayrun shekara ta 1979.

Wannan dai yana daga cikin Jerin shirye-shiyen da aka tsara na bukukuwan cika shekaru 46 da nasarar juyin juya halin musulunci a kasar Iran. Wanda za’a kamala shi a ranar 22 ga watan Bahman na shekara ta 1403.

Ana fara bukukuwan cika shekaru 46 da nasarrar juyin juya halin musulunci a kasar Iran ne tun ranar 1 ga watan Farairu 2025 a duk fadin kasar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: shekaru 46 da

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Ukraine Ya Sami Tarba Mai Kyau A Burtaniya Bayan Cacan Baki Mai Zafi Da Trump

Shugaban kasar Ukrain Volodomyr Zelesky ya samu tarba mai kyau a kasar Burtaniya bayan ya isa birnin London a jiya Asabar kuma bayan cacan baki mai zafi da yayi da shugaban Amurka Donal Trump a fadar White House dangane da yakin Ukraine.

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya bayyana cewa shugaba Zeleski ya gana da firaiministan kasar Burtania Keir Starmer, wanda ya yaba masa kan yadda ya tsayawa kasarsa da kuma kasashen turai a gaban shugaban Amurka Donal Trump da mataimakinsa a ranar jumma’an da ta gabata.

Labarin ya kara da cewa shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya zanta da shuwagabannin biyu, wato Trump da kuma Zeleski don kwantar da hankali.

A yau Lahadi ce za’a gudanar da taro na musamman kan abinda ya faru tsakanin Zelesky da Trump da kuma makoman kasar Ukraine a yakin da take fafatawa da Rasha tun shekaru 3 da suka gabata.

Sauran shuwagabannin kasashen Turai sun yabawa Zelesky da yadda ya tsayawa kasarsa da kasa kasashen turai a tattaunawarsa mai zafi da manya-manyan Jami’an gwamnatin Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Jana’izar Shugaban Kasar Namibia Da Ya Samo Mata ‘Yanci
  • Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
  • Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan
  • Shugaban Kasar Ukraine Ya Sami Tarba Mai Kyau A Burtaniya Bayan Cacan Baki Mai Zafi Da Trump
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • Xi Ya Jaddada Ciyar Da Shirin Kasar Sin Mai Kwanciyar Hankali Zuwa Babban Mataki
  • Iran Ta Zama Zakara A Damben Gargajiya Ta 2025 UWW Wanda Aka Gudanar A Kasar Albaniya
  • Wasu Kasashen Musulmi Sun Fara Azumin Ramadana A Yau Asabar, Yayin Da Wasu Za Su Fara A Gobe Lahadi
  • Noman Rani: Tinubu Ya Amince Da Fadada Madatsun Ruwa 12 A Nijeriya