Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Bayyana Matakan Da Amurka Zata Bi Don Kyautata Dangantaka Da Iran
Published: 1st, February 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Aragchi yana bayyana matakan da sabuwar gwamnatin Amurka zata dauka idan har tana son sake samun yardar samun yardar kasar Iran.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a lokacinda yake hira ta musamman da tashar talabijin ta Al-jazeera ta kasar Qatar a birnin Doga.
Ministan ya kara da cewa gwamnatocin Amurka da suka shude daga ciki har da gwamnatin Trumps suka yi a baya musamman ficewarta su daga yarjeniyar JCPOA.
Abbas Argchi ya bayyana cewa abu mafi muhimmanci wanda dole ne Amurka ta yi idan tana son jawo hankalin iran dangane da tattaunawa da ita shi ne sako kudaden ta masu yawa wadanda ta hana a yi amfani da su a wurare da dama a duniya.
Ministan ya ce wannan yana iya zama mataki na faro wanda gwamnatin Amurka zata iya dauka idan tana son haka.
Kafin haka dai gwamnatin sabuwar gwamnatin Amurka tana ganin tattaunawa da kasar Iran ita, tana ganin hanyar da zata da ita, don warware matsaloli daban-daban da suke tsakaninsu. A wannan karon.
Sannan ya kara da cewa idan har tana son al-amura su tafi mata yadda take so, ya kasance tattaunawar ta shirin nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya ce kadai za’a yi magana a kansa, kada ta hana da wasu al-amura, musamman rawar da irin take takawa a yankin Asiya ta kudu.
Kafin haka dai gwamnatin Donal Trumps a zagayen na farko ne ta fidda Amurka daga yarjeniyar JCPOA wacce aka kulla da gwamnatin Obama a shekara ta 2015, kuma ta fice daga cikinta a shekara ta 2018 sannan ta sake dorawa kasar takunkuman tattalin arziki mafi muni a tarihin kar wadanda suke aiki har yanzun.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Mayar Da Martani Ga Shirin Japan Na Aiwatar Da Matakan Hana Fitar Da Kayayyaki Zuwa Sin
Yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar kasuwanci ta Sin ya amsa tambayoyin ‘yan jarida game da shirin Japan na aiwatar da matakan hana fitar da kayayyaki zuwa Sin, ciki har da semiconductor.
Kakakin ya bayyana cewa, shirin bangaren Japan na aiwatar da matakan, zai kawo cikas ga tsaro da kwanciyar hankali na tsarin masana’antu, da gurgunta mu’amalar kasuwanci na yau da kullum dake tsakanin kamfanoni, da kuma lalata muradun kamfanonin kasashen biyu.
Dangantakar Cinikayya Da Sin Ta Budewa Afrika Kofar Samun Ci Gaba Ana ɗar ɗar Kan Mutuwar Sojoji Bayan Da Mota Ta Kwace A LegasSin na fatan kasar Japan za ta ji ra’ayoyin masana’antu, ta kuma gaggauta gyara ayyukan da ta yi bisa tushen kiyaye ka’idojin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa, da moriyar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da Sin.
Bugu da kari, ya ce kasar Sin za ta dauki matakan kiyaye hakki da moriyarta.(Safiyah Ma)