Leadership News Hausa:
2025-04-07@21:10:47 GMT

Aston Villa Na Neman Ɗaukar Marcus Rashford A Matsayin Aro 

Published: 1st, February 2025 GMT

Aston Villa Na Neman Ɗaukar Marcus Rashford A Matsayin Aro 

Aston Villa na ɗaya daga cikin ƙungiyoyi da dama da ke son ɗauko ɗan wasan gaba na Manchester United Marcus Rashford, ɗan wasan mai shekaru 27 bai taka leda a United ba tun lokacin da babban kocin ƙungiyar Ruben Amorim ya ajiye shi a wasan Manchester derby a ranar 12 ga watan Disamba.

Amorim ya ce a ranar Laraba yana jin ƙungiyarsa za ta fi kyau da Rashford a ciki, amma ɗan wasan bai cika ƙa’idojin da ya buƙata ba, wakilan Rashford sun gana da wasu manyan ƙungiyoyin Turai a cikin ‘yan makonnin da suka gabata a ƙoƙarinsu na ganin ya bar Manchester.

Mece Ce Matsalar Manchester United? AC Milan Ta Kammala Ɗaukar Kyle Walker Daga Manchester City A Matsayin Aro

Majiyoyi da dama sun tabbatar da cewa har yanzu ba a yanke shawarar makomar Rashford ba, har yanzu Manchester ba ta bayar da damar sayen Rashford ba amma kuma akwai yiwuwar ta bari ya tafi a matsayin aro, Villa na ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da ke zawarcin ɗan wasan na Ingila, Rashford yana ɗaya daga cikin manyan masu karɓar albashi a United, tare da albashi sama da £300,000 a mako.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Marcos

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin APC na Ogun, Tunde Oladunjoye, ya rasu

Mai magana da yawun jam’iyyar APC a Jihar Ogun, Tunde Oladunjoye, ya rasu.

Ya rasu ne a ranar Juma’a, 4 ga watan Afrilu, 2025, yayin da yake jinya a ƙasar waje kan wata rashin lafiya da ba a bayyana ba.

An haramta wa Akpabio da Natasha tattaunawa da manema labarai Yadda aka yi jana’izar Dokta Idris Dutsen Tanshi a Bauchi

Iyalansa sun tabbatar da rasuwarsa a cikin wata sanarwa, inda suka bayyana shi a matsayin mutumin kirki kuma jajirtacce.

Gwamnan Jihar Ogun, Dapo Abiodun, wanda Oladunjoye ke yi wa aiki a matsayin mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, ya ce rasuwarsa babban rashi ne.

Ya ce Oladunjoye mutum ne mai kishin jam’iyya, jajirtacce, kuma ya taka rawar gani wajen tallata APC a jihar.

Za a sanar da lokacin jana’izarsa daga baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fulham ta doke Liverpool bayan wasa 26 a jere ba tare da rashin nasara ba
  • Yau Ta Ke Manchester Dabi 
  • Ɓarawo ya haɗiye ɗan kunnen Naira biliyan ɗaya
  • De Bruyne zai yi bankwana da Manchester City a ƙarshen kaka
  • Pezeshkian ya soki barazanar Amurka kan kasarsa game da tattaunawar nukiliya
  • Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya (2)
  • Kofin Duniya: Kocin Nijeriya Na Fatan Matashin Ɗan Wasan Arsenal Nwaneri Ya Wakilci Ƙasar
  • Bruno Fernandes Ba Na Sayarwa Ba Ne – Ruben Amorim
  • Pezeshkian: Iran ba ta neman yaki da kowace kasa
  • Kakakin APC na Ogun, Tunde Oladunjoye, ya rasu