Aminiya:
2025-02-01@15:55:57 GMT

Muna da ƙarfin aljihun ɗaukar nauyin Taron Al-Ƙur’ani —Sheikh Bala lau

Published: 1st, February 2025 GMT

A wannan hirar, Shugaban Kungiyar Jama’atu Izalatuil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Sheikh Abdullahi Bala Lau, ya yi magana game da cece-ku-ce kan ɗaukar nauyin wani taron Al-Ƙur’ani da aka shirya.

Da yake magana jim kaɗan bayan wata lacca ta musamman a sakatariyar JIBWIS ta ƙasa da ke Abuja a wannan makon, shugaban ya bugi ƙirji da cewa al’ummar Musulmi na da kuɗin da za su iya shirya taron.

Aminiya: Za mu ka yi mana bayani kan mahimman abubuwa game da taron Al-Kur’ani da aka shirya?

Amsa: Taron Al-Qur’ani mai zuwa a ranar 22 ga Fabrairu ya shafi gabatar da karatun Al-ƙur’ani mai girma, inda makaranta da mahaddata za su taru a bisa jagorancin Sarkin Musulmi na Sakkwato. Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya ce ta shirya wannan taro. An gayyaci duk ƙungiyoyin Musulunci; kuma muna cikinsu.

Don haka, muna ganin ya wajaba a gare mu mu gaya wa dubban masu kallo da mabiyanmu cewa wannan shi ne manufar wannan taro da zai tattar makaranta da mahaddata Al-ƙur’ani Mai Girma ta hanyar Tsangaya da waɗanda suka haddace ta hanyar Musabaka.

Mun gane cewa babu wata hanya da za ta haɗa su wuri ɗaya don su fahimci juna, su gabatar da takardu da wayar da kai duk da cewa dukkanmu muna da manufa ɗaya da za mu cimma, wato Al-Ƙur’ani ɗaya ne kawai; Annabinmu Muhammad (SAW) ɗaya ne; muna fuskantar Alƙibla ɗaya; muna da littafi ɗaya, al’umma ɗaya; to yaya za mu haɗu?

A cikin ƙungiyarmu, idan muna son shirya wani abu, muna da hanyoyi da yawa na aika saƙonni ga mabiyanmu. Amma muddin akwai haɗin kai, muna son samun haɗin kan al’ummar Musulmi; kuma wannan shi ne mafi muhimmanci. Sarkin zai jagoranci taron. Ya kira mu kuma mun amsa. Muna cikin wannan shirin.

Amma akwai rashin fahimta da yawa game da wannan taron; me ya sa?

’Yan siyasa sun shigo shi ya mutane suna tunanin cewa gwamnati ce ta shirya taron. Ba gaskiya ba ne. Na gaya muku wa ya shirya shi; mu ne, ƙungiyoyin Musulunci.

Ina kuke a lokacin da muka shiga tsakani kan batun Jamhuriyar Nijar da Ƙungiyar Tattalin Arziƙin Afirka ta Yamma (ECOWAS)? Shin ba malaman ba ne suka haɗu suka shiga tsakani kuma zaman lafiya ya samu tsakanin Najeriya da Nijar? Wannan shiga tsakani yana tasiri mai yawa; ya haifar da wayar da kai sosai tsakanin Najeriya da Nijar kuma ya kawo sauyi da yawa.

Don haka, a matsayinmu na malaman Musulunci, muna jin cewa wajibi ne a garemu mu sami wurin da za a cike gibin da ke tsakanin makaranta Al-ƙur’ani da mahaddata ta hanyar Tsangaya da waɗanda suka yi ta hanyar Musabaka kuma suka ƙara koyon Tajweed.

Muna son rufe wannan giɓi don su iya haɗuwa su fahimci juna; kuma a ƙarshe, za a gabatar da takardu.

Yaya kuke shirin tara kuɗin wannan taron?

Al’ummar Musulmi za su iya ɗaukar nauyinsa. Na gaya maka, a ƙarƙashin ƙungiyarmu muna da masallatan Jumu’a sama da 15,000 kuma idan muka ce kowane masallaci ya bayar da gudummawar N10,000, kuna aka  ninka shi sau 15,000, nawa ke nan?

Akwai masu fatan alheri da yawa waɗanda suke son bayar da gudummawa a matsayin domin neman lada saboda Allah. Don haka al’ummar Musulmi na da hanyoyin kawo gudummawa ta hanyar irin wannan taron.

Mutane da yawa sun dage cewa akwai mai ɗaukar nauyi na musamman na taron; me za ka ce?

Babu mai ɗaukar nauyi na musamman na wannan taro. Mutane kawai suna faɗin abin da suke so, amma a yadda muka sani, muna neman gudummawarku. Don Allah ku kawo gudummawarku kuma ni ma zan kawo tawa.

Kuna tsammanin al’ummar Musulmi ba za su iya ɗaukar nauyin irin wannan shirin ba ne? Idan wannan shirin zai ci Naira biliyan daya ko biyu, a ƙarƙashin JIBWIS, a cikin wata guda za mu iya tara har zuwa N600 miliyan ko biliyan ɗaya. Me kuke tunani game da sauran ƙungiyoyi? Ba za su iya yi ba? Idan gwamnati tana son shiga ta bayar da gudummawa, wa zai ce a’a?

Shin mu ba wani ɓangare na gwamnati ba ne? Mu ne muka kawo gwamnati kan karagar mulki, don haka muna da ’yancin mu nemi ta ɗauki nauyi ko ta ba da taimako tunda suna son zaman lafiya da jituwa su mamaye a Najeriya.

Me ya sa wannan taron ke zuwa a lokacin da ake fama da matsanancin ƙunci a ƙasar?

Ai ba a kan ƙunci ba aka shirya ahi, akwai wasu tarurruka da aka gudanar a wannan lokacin. Me ya sa ba za mu iya gudanar da wannan taron ba? Lokacin ƙunci lokaci ne na wayar da kan al’ummar Musulmi don su fahimta. Ƙuncin ya fito daga wa? Daga Allah; kuma idan ka sami kanka cikin jin daɗi, ya fito daga wa? Daga Allah. Don haka, a koma ga Allah. Muna buƙatar ci gaba da karanta Al-ƙur’ani mai girma da kuma yaɗa tauhidi. Kuma idan ka yi imani da Allah, zai yi maka abubuwa da yawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Al ummar Musulmi al ummar Musulmi wannan taron

এছাড়াও পড়ুন:

Cece-kuce Ya Barke Kan Shirin “Kur’anic Convention”

“Kazalika, wasu kuma da suke da haddar Alkur’anin; ciki har da wadanda suka rubuta shi da hannunsu, ba a samun wata mahada da ake haduwa. Wannan dalili ne ya sa in sha Allahu, muka sanya kafin watan Azumi; dukkanin kungiyoyin addinin musulunci, babu abin da zai iya hada mu kamar Alkur’ani. Alkur’ani ya hada mu, ba mu da banbanci da kowa, domin kowa ya yarda da shi, in ji shi.

“Don haka, muna sa ran mahaddata Alkur’ani sama da 30,000, za su shigo garin Abuja, daf da sati guda kafin Ramadan a yi ‘Festival’ na Alkur’ani, mu ji sautuka daban-daban; domin kuwa akwai sautuka irin na Yarbawa, wanda idan suna yi suna jin dadi tare da motsawa, akwai kuma sauti irin na Larabawa, wanda shi ma idan an ji; ana motsawa da kuma sauti irin na su Alaramma, wato na gargajiya”, in ji Bala Balau.

Wadannan jawabai na Shugaban Kungiyar Izala, sun yi matukar tayar da kura tare da haifar da cece-kuce, domin kuwa da dama daga cikin mabiya kungiyar, sun yi wa shugaban nasu tawaye tare da bidi’antar da shirin.

Haka nan ma, a tsagin Darikar Tijjaniyya; Halifan Sheik Dahiru Usman Bauchi, Sheik Ibrahim; shi ma ya yi karin bayani a kan wannan biki da aka shirya na ‘Kur’an Festibal’, inda ya bayyana shirin da cewa, an kawo shawarar shirya shi ne; domin yin godiya ga Allah SWT, da ya azurta Nijeriya da mahaddata Al’kur’ani fiye da sauran dukkanin kasashen duniya.

“Wannan dalili ne yasa, wasu ‘yan’uwa suka kawo shawarar aiwatar da wannan biki, domin yi wa Allah godiya da wannan baiwa da ya yi wa Nijeriya. Shi yasa muke so in sha Allahu, za a tara mahaddata Alkur’ani a Abuja, ranar 22 ga watan Fabrairu, 2025, wanda ya yi daidai da 23 ga watan Sha’aban na shekara ta 1446, a Sitadiyom ; domin aiwatar da wannan biki”, in ji Sheik Ibrahim.

Har ila yau, Sheik Sani Yahya Jingir, guda cikin manyan jagororin Izala a Nijeriya, shi ma ya soki wannan shiri na ‘Kur’anic Festival’, da ake kokarin shiryawa, inda ya yi kira ga wadanda ragamar ke hannunsu, da sunan ‘yan damfara.

Jingir ya bayyana cewa, da dama daga cikin wadanda ake so a gayyata daga cikin mahaddata kur’anin, bai yadda da musuluncinsu ba, domin kuwa ya kira su da sunan Bokaye da Matsafa.

“Masu zagin Alkur’ani, suna auna shi da turare; su ne masana kur’ani, wadanda a gidansu aka fito aka zagi kur’anin a Kano; aka kuma yanke hukuncin kisa ta ridda a kansu, su ne masu haduwa su karanta Alkur’anin? Ko kuwa masu karanta kur’anin suna kada ganga suna watayawa tare da rausayawa, su ne masu karanta kur’anin?” tambayar da Sheik Jingir ya yi.

Shi ma, wani mai fashin baki a kan al’amuran yau da kullum a Nijeriya, Sani Ahmad Zangina, ya yi nuni da cewa; babu wani abu a cikin wannan shiri na ‘Kur’anic Festival’, illa zallar siyasa; wanda kawai malamai suka karbo kwangilarta, domin cika aljihunansu.

“Babban abin lura a nan shi ne, tunda an ce shiri ne da ya hada dukkanin alarammomin Nijeriya, idan ka kawo ‘yan Izalar Jos da na Kaduna, ‘yan Shi’a, ‘Yan Kala-kato da kuma sauran ‘yan Dariku, idan aka tashi yin sallar azahar a wajen taron, wane ne zai yi limanci?, tunda dai babu yadda za a yi a ce an yi taron har an tashi ba a yi sallah ba.

“Don haka, wannan taro na siyasa ne; babu komai a cikinsa idan ba siyasa ba. Saboda haka, mu abin da muke kallo shi ne, a tsaya a yi abin da ya kamata, domin kuwa a dan sanin da muke da shi; muna ganin ba daidai ba ne a yi wasa da wannan littafi na Allah, musamman wajen sayar da ayoyinsa, saboda wani abu na duniya”.

“Don haka, batun wannan ‘Kur’anic Festival’; akwai ayar tambaya a ciki, ya kuma kamata malamai su rike girmansu da mutuncin da suke da shi, musamman a irin wannan lokaci da zarge-zarge suka yawaita a kansu”, in ji Zangina.

Ya ci gaba da cewa, Alarammomin da ake so a dauko a kawo Abuja daga jihohinsu, musamman daga Arewacin Nijeriya, yankunan da suke fama da yunwa da matsalolin tsaro, kyautuwa ya yi a taimako, ba wannan yaudarar ba.

“Maimakon a ce kowane Alaramma da za a dauko daga jiharsa a kawo shi Abuja, idan misali Naira miliyan daya za a ba shi; mai zai hana ba za a ba shi kudin, amma ya yi zamansa a garinsu ya yi addu’ar a can ba, maimakon sai ya zo Abuja ya kashe akalla dubu dari ko dari biyu? Don Allah, kada mu yaudari kanmu ko mu yaudari Allah, tunda shi ne mafi sanin abin da yake ranmu”, in ji shi.

Har ila yau, ya kara da cewa, wannan taro na ‘Kur’anic Festibal’, ba shi da wata fa’ida; illa ma cutarwa, domin kuwa an samu zubewar mutunci, musamman daga wurin malaman da ke kan gaba-gaba wajen ganin an yi taron.

Ya sake bayyana cewa, ko da ba a zargin akwai siyasa a cikin wannan taro, a irin wannan lokaci na siyasa da ake bukatar jama’a, ku san kowa zai iya kallon taron da ido daya. Saboda haka, magana ta gaskiya ita ce, tunda an ce hadin kai ake nema; kada a ce saboda Al’kur’ani za a zo a yi taro, sannan kuma gobe a zo ana barranta tare da tsinewa juna, a cewar Zangina.

Dakta Ahmad Gumi, shi ma ya tofa albarkacin bakinsa a wannan dambarwa da ke ci gaba da daukar hankulan al’umma ta hanyar sukar shirin na ‘Kur’anic Festival’, inda ya bayyana shi a matsayin wata sabuwar bidi’a da aka bullo da ita.

“Kur’ani, ba ya bukatar biki; domin kuwa, zuciyarmu kullum cikin bikin kur’ani take, tun daga safe da za ka tashi ka yi ‘yan nafilfilolinka; idan mai yin nafilar ne, ko ka yi raka’atanil fijir, ka yi sallar asubahi, ka yi azakar, ka yi azahar, ka yi la’asar, ka yi magariba har zuwa sallar isha’i, wannan na nuna cewa; dukkanin rayuwarka Alkur’ani ce.”

“Saboda haka, ya kamata malamai su rika yin shawara; su kuma daina yin gaggawa, duk da cewa; da yawansu ba su san yadda aka kafa Sunnah ba. Sannan, wadannan malamai suna da rauni guda biyu, na farko; idan suna gaban shugaba da zarar sun fahimci ya karkata a kan wani abu da yake so, nan take sai su fara karanto ayoyi da hadisan da suka karkata a kan abin da shugaban yake so”, in ji Gumi.

Haka zalika, rauni na biyu kuma da malaman ke da shi a cewar Sheik Gumin shi ne, ga masu kudi, nan ma da zarar sun fahimci hankalin mai kudi ya karkata kan wani abu da yake so, nan take za su fara jawo ayoyi da hadisai, domin su kara karfafa shi ta yadda zai karfafi wannan abu da yake so.

“Babban abin lura a nan shi ne, ana so a kashe biliyoyin kudi a wajen wannan taro ta hanyar tara wadannan Mahaddata, domin su zo kowa ya baje kolinsa ko gwanintarsa. Don haka, ya kamata a san cewa, ka fito ka nuna kai Mahaddaci ne ma kadai, wannan raina Alkur’ani ne.

“Sannan kudaden da za a kashe, mai zai hana a je a gyara tsangayoyin da muke da su, ko kuma shi kansa malamin tsangayar a saya masa gida, domin ya ji dadin ci gaba da koyar da Alkur’anin? Saboda haka, wannan kirkirarriyar bidi’a ce. Sannan kuma, muna fata kungiyar Izala za ta rika yin shawara kafin aiwatar da duk wani abu da ya taso.

Kazalika kuma, ina kyautata zaton cewa; wannan taro ba siyasa ba ce, illa kawai dai wani mai kudi ne da yake ganin kamar yin wannan wani abu ne mai kyau, amma kuma babu wanda ya ankarar da shi tare da fada masa gaskiyar cewa, yin hakan ba daidai ba ne, in ji Gumi.

A gefe guda kuma, kamar yadda ‘yan Izala ke ci gaba da yi wa ‘yan’uwansu raddi kan wannan shiri na ‘Kur’anic Festival’, shi ma Imam Ali Abulfatahi, ya yi wa Sheik Ibrahim Dahiru Bauchi nasa raddin, a matsayin kira da kuma nasiha ga shugabannin Darikar Tijjaniya, wanda ya bayyana cewa; su ne alkiblarsu a nan gaba.

”Idan wannan ta kasance ita ce tafiyar Darika, to kuwa ko shakka babu; a nan gaba hoton Darika ba zai yi kyau ba, domin kuwa; iyayenmu da sauran Shehunanmu, ko kadan ba wannan ce matafiyarsu ba. Saboda haka, Ya Ibrahim; a irin wannan matafi da ake ciki a Darika, ana bukatar shawara ko tuntuba, domin a Nijeriya akalla akwai ‘yan Darikar Tijjaniyya sama da miliyan sittin zuwa saba’in, Almajiran Shehu Tijjani da Shehu Ibrahim.”

“Akwai maganarka da na ji kana cewa, a Darika kowa ya san na gaba da shi; babu shakka wannan gaskiya ka fada, shi yasa yau babu wanda zai fito a Darika ya ce shi ne shugaba, illa kawai dai kowa ya san na gaba da shi, sannan Allah ya sanya wa ‘yan Darikar tsananin biyayya ga na gaba da su; shi yasa farkon Darika ya zama ladabi, tsakiyarta ladabi, haka nan ma karshenta ladabi; wannan ne yasa abubuwa da dama suke faruwa da mu sakamakon wannan ladabi da muke da shi.

“Saboda haka, babu yadda za a yi ka zauna a Kasar Ingila, duk kuwa da irin yawan wadannan al’ummar da muke da su a Darika, kai kadai ka wakilce su; su sama da kimanin miliyan 60 zuwa 70, ba tare da ka shawarci kowa ba; ka yi garkuwa da Maulana Sheik Dahiru Usman Bauchi, ka ce shi ne ya fadi haka, saboda ka san cewa dole ne mu ce mun bi, tunda a dukkanin fadin wannan kasa ba mu da tamkarsa.

“In dai kuwa za a ci gaba da tafiya a haka, babu yadda za a yi Darika ta dunkule wuri daya, sau da dama idan aka kawo sukar Alhaji Ibrahim, dan maulana Sheik Dahiru Usman Bauchi, na kan ce; a yi masa uzuri, domin dama ya samu. Sannan, kashi 85 cikin 100 na ‘ya’yan Shehunanmu, duk wanda ya samu irin wannan dama, ko shakka babu; zai yi amfani da ita, duk da cewa ba a taru an zama daya ba, amma dai ya kamata mu sani duk abin da yake da farko, yana da karshe.”

Abulfatahi ya ci gaba da cewa, yanzu Sufanci da Darika sun yi gabas, su kuma sun yi yamma; saboda irin abubuwan da suke faruwa marasa dadi na son kai ko son zuciya. Babu tsoron Allah yanzu, babu zuhudu da kyawawan dabi’un da aka kafa a Darika ko Sufanci, wannan shi ne martanin na Abulfatahi ga Sheik Ibrahim Dahiru Usman Bauchi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aston Villa Na Neman Ɗaukar Marcus Rashford A Matsayin Aro 
  • An Kama Miyagun Kwayoyi Kan Hanyar Zuwa Birtaniya A Filin Jiragen Saman Legas
  • Yadda Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass ya yi wa Tinubu addu’ar nasara
  • Kissoshin Rayuwa Imam Hassan (a) 09
  • Gwamna Buni ya zama Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Tafkin Chadi
  • Rikicin Shugabanci Na Barazana Ga Babban Taron Jam’iyyar PDP
  • Tunawa Da Ranar Wadanda Aka Yi Wa Kisan Kiyashi: Majalisar Dinkin Duniya Ta Wayar Da Kan Dalibai A Abuja
  • An Dakatar Da Bin Uthman Daga Limancin Masallacin Sahaba, DSS Ta gayyace shi
  • Cece-kuce Ya Barke Kan Shirin “Kur’anic Convention”