AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin Rukuni
Published: 1st, February 2025 GMT
Yadda aka raba jadawalin AFCON 2025:
Rukunin farko: Morocco, Mali, Zambia, Comoros — Rukuni na biyu: Egypt, South Africa, Angola, Zimbabwe—- Rukuni na uku: Nigeria, Tunisia, Uganda, Tanzania
Rukuni na hudu: Senegal, DR Congo, Benin, Botswana
Rukuni na biyar: Algeria, Burkina Faso, Ekuatorial Guinea, Sudan
Rukuni na shida: Cote d’Iboire, Cameroon, Gabon, Mozambikue
.এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kwara ta fara yi wa maniyyata rigakafin cututtuka kafin gudanar da aikin Hajji na shekarar 2025.
Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin rigakafin da aka gudanar a harabar hukumar da ke Ilori, shugaban hukumar, Alhaji Abdulsalam Abdulkadir, ya bayyana rigakafin a matsayin wani sharadi da ya zamto wajibi ga dukkan Alhazai bisa umarnin gwamnatin Saudiyya.
Ya ce yin rigakafin yana da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da lafiyar Alhazai a lokacin gudanar da aikin Hajji.
A cewarsa, an shirya shirin rigakafin ne domin hana yaduwar cututtuka da kuma tabbatar da cewa Alhazai sun samu lafiya da kwanciyar hankali yayin aikin Hajjin.
Alhaji Abdulkadir ya bayyana cewa za a fara jigilar rukuni na farko na Alhazai daga jihar zuwa ƙasar Saudiyya ranar 12 ga watan Mayu.
Shugaban hukumar ya ƙara da cewa za a kammala aikin rigakafin ne ranar Laraba 30 ga watan Mayu, sannan kuma za a fara raba tufafi da jakunkunan tafiya nan take.
Alhaji Abdulkadir ya yi kira ga maniyyatan da su kammala duk shirye-shiryen lafiyar jiki da na tafiya cikin lokacin da aka kayyade domin samun nasarar aikin Hajjin ba tare da wata tangarda ba.
Ali Muhammad Rabi’u