Leadership News Hausa:
2025-04-09@00:50:41 GMT

AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin Rukuni

Published: 1st, February 2025 GMT

AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin Rukuni

Yadda aka raba jadawalin AFCON 2025:

Rukunin farko: Morocco, Mali, Zambia, Comoros — Rukuni na biyu: Egypt, South Africa, Angola, Zimbabwe—- Rukuni na uku: Nigeria, Tunisia, Uganda, Tanzania

Rukuni na hudu: Senegal, DR Congo, Benin, Botswana

Rukuni na biyar: Algeria, Burkina Faso, Ekuatorial Guinea, Sudan

Rukuni na shida: Cote d’Iboire, Cameroon, Gabon, Mozambikue

.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It Back

Ƙungiyar Take It Back ta ce zanga-zangar da za gudanar a yau babu gudu babu ja da baya domin nuna adawa da dokar ta-baci da aka sanya a Jihar Ribas da kuma abin da ta kira cin zarafin bil’adama da kuma amfani da dokar ta’addancin yanar gizo ba bisa ka’ida ba.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta gargaɗi masu shirin yin zanga-zanga ranar Litinin 7 ga watan Afrilu a faɗin ƙasar su sake tunani domin a ranar ce ‘yan sandan ƙasar suke bukukuwa domin nuna gudunmawar da suka bayar don ci-gaban Nijeriya.

Rundunar ta ce zanga-zangar da wata ƙungiya mai suna “Take It Back” ta shirya tana zuwa ne a lokacin da bai dace a yi zanga-zanga a ƙasar ba.

Wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan ƙasar, Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ta ce rundunar ba ta adawa da ‘yancin ‘yan ƙasar na taruwa da yin gangami da kundin tsarin mulkin Nijeriya ya ba su.

Sai dai kuma sanarwar ta ce rundunar na fargaba game da burin waɗanda suka shirya yin zanga-zangar rana ɗaya da ranar da aka ware domin yaba wa irin jajircewa da sadaukar da kai na ‘yan sandan Nijeriya.

“Bisa ga ingatattun ɗabi’un da ƙasashen duniya ke bi wajen yabawa da nasarorin ‘yan sandansu, gwamnatin Nijeriya ta ɗauki matakin ayyana ranar 7 ga watan Afrilu a matsayin ranar ‘yan sandan Nijeriya,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa bikin zai samu halartar baƙi daga ciki da wajen ƙasar daga fannoni daban-daban, ciki har da sufeto janar na ‘yan sandan ƙasashen ƙetare da kuma jami’an diflomasiyya.

“Dalilin gudanar da zanga-zanga a irin wannan ranar abin dubawa ne kuma a iya cewa wani mataki ne na ɓata sunan ‘yan sandan Nijeriya da ƙasar ma baki ɗaya,” in ji sanarwar.

“Saboda haka rundunar ‘yan sandan Nijeriya tana bai wa waɗanda suka shirya wannan zanga-zangar shawarar janyeta saboda lokacin bai dace da ita ba kuma tana da manufar aikata ɓarna,” in ji Olumuyiwa.

Sai dai duk da wannan gargaɗi, ƙungiyar ta Take It Back ta ce tana nan kan bakarta domin nuna adawa kan abin da ta kira mulkin kama karya da gwamnatin Shugaba Tinubu ke yi a ƙasar nan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya: An gudanar da zanga-zangar adawa da wasu shirye-shiryen  gwamnati
  • Lakurawa Sun Kashe ’Yan Sa-kai 13 A Wani Sabon Hari A Kebbi
  • HOTUNA: Yadda zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta gudana a wasu biranen Nijeriya
  • Saudiyya ta musanta hana ’yan Nijeriya biza
  • JAMB Ta Bankaɗo Jabun Takardun Shaidar Kakammal Sakandire 585 A Shekarar 2025
  • Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It Back
  • Wani Kwararre Ya Bukaci A Rungumi Fahasar Zamani Don Bunkasa Aikin Noma A Nijeriya
  • Arzikin Nijeriya Ya Habaka Zuwa Naira Tiriliyan 22.61 A Zangon Karshe Na 2024 – CBN
  • Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025
  • Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025