Leadership News Hausa:
2025-03-04@01:00:02 GMT

Van Rompuy: Ya Kamata A Kiyaye Cudanya Tsakanin Mabambantan Al’adu

Published: 1st, February 2025 GMT

Van Rompuy: Ya Kamata A Kiyaye Cudanya Tsakanin Mabambantan Al’adu

Wakilin CMG ya yi hira da tsohon shugaban majalisar nahiyar Turai, kuma tsohon firaministan kasar Belgium, Herman Van Rompuy, a kwanan baya, inda tsohon shugaban ya nanata bukatar karfafa cudanya tsakanin al’adun bangarorin yammaci da gabashin duniya.

Herman Rompuy ya ce, ta hanyar cudanya, kowa zai iya koyon sabbin dabarun da yake bukata, kana za a iya tabbatar da fahimtar juna.

A daura da haka, idan an yi watsi da damar cudanya da tattaunawa, to, tabbas za a samu abkuwar rikici da arangama, har ma zai kai ga barkewar yake-yake.

Aston Villa Na Neman Ɗaukar Marcus Rashford A Matsayin Aro  AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin Rukuni

Dangane da shawarar raya “Ziri Daya da Hanya Daya” da kasar Sin ta gabatar, Mista Rompuy ya ce, ana bukatar tabbatar da saukin jigilar kayayyaki tsakanin kasashe daban daban, gami da ingancin cinikin duniya, ganin yadda suka jibanci wadatar al’ummun kasashen duniya. Saboda haka, yana goyon bayan duk wani matakin da zai amfanawa karfafar hadewar sassan duniya.

Ban da haka, tsohon dan siyasan na nahiyar Turai ya yi tsokaci kan shawarwarin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, dangane da yunkurin tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da tsaro, da ingancin cudanyar al’adu a duniya, inda ya ce, shawarwari sun nuna burikan da ake neman cimmawa a kasashe masu sukuni, da wadanda ke kan hanyar tasowa baki daya. Ya ce, dukkan kasar Sin da kasashen Turai za su iya samar da gudunmowa ga yunkurin cimma wadannan manyan burika masu muhimmanci. (Bello Wang)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila

Shugabannin kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombia sun jaddada aniyarsu ta hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila amfani da tashar jiragen ruwansu, a daidai lokacin da gwamnatin kasar ke ci gaba da aiwatar da kisan kare dangi a zirin Gaza.

“Za mu hana jiragen ruwa da ke dauke da kayan aikin soji zuwa Isra’ila amfani da tashoshin jiragen ruwanmu; kamar yadda,” Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, Firayim Ministan Malaysia Anwar Ibrahim da Shugaban Colombia Gustavo Petro suka rubuta a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da mujallar harkokin waje ta buga a wannan makon.

Sun jaddada cewa yakin da Isra’ila ke yi a Gaza ya fallasa gazawar tsarin kasa da kasa, tare da yin kira da a kawo karshen rashin hukunta dokokin kasa da kasa da Isra’ila ke yi.

Malesiya da Colombia na daga cikin kasashen da suka goyi bayan korafin kisan kiyashin da kasar Afrika ta kudu ta kai kan Isra’ila a kotun duniya ta ICJ.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Namun Dajin Kasar Sin Sun Karu Yadda Ya Kamata
  • Tawagar ECOWAS Ta Fice Daga Guinea-Bissau Bayan Barazana Daga Shugaban Kasar
  • Kasancewar Zaman Lafiya Na Dogon Lokaci Tsakanin Sin Da Amurka Abu Ne Da Ya Zama Wajibi
  • Abubuwan da ya kamata a sani game da azumin watan Ramadana
  • Shugaban Kasar Ukraine Ya Sami Tarba Mai Kyau A Burtaniya Bayan Cacan Baki Mai Zafi Da Trump
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • Sin Ta Kiyaye Girmama Kasashen Tsibirai Na Yankin Tekun Pasifik
  • Bayan Kwana 22, Tsohon Shugaban NYSC Tsiga Ya Kuɓuta A Hannun Ƴan Bindiga
  • Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House