Sojojin Sudan Sun Kwace Iko DaBirnin Umm Rawaba A Jihar Kordofan Ta Arewa
Published: 1st, February 2025 GMT
Sojojin Sudan sun kwace iko da wani birni da ke arewacin Kordofan daga hannun ‘yan tawayen kasar na Rapid Support Forces
Rundunar sojin Sudan ta sanar da cewa ta sake kwace iko da birnin Umm Rawaba, birni na biyu mafi girma a arewacin jihar Kordofan da ke kudancin kasar daga hannun dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces.
A cikin wata sanarwa da rundunar sojin Sudan ta fitar ta ce: Godiya ta tabbata ga Allah da yardarSa, sojojin sun tsarkake birnin Umm Rawaba daga hannun mayakan dakarun kai dauki gaggawa da sojojin hayarsu, tare da janyo musumunanan hasarori masu yawa.
A cewar shafin yanar gizo na Arabi 21, Dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces sun mamaye birnin Umm Rawaba ne tun daga watan Satumban shekara ta 2023, wanda ke da tazarar kilomita 145 daga birnin Al-Abyadh, babban birnin jihar Kordofan ta Arewa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamna Lawal ya Yaba Wa DSS Kan Bankaɗo Makamai A Jihar Zamfara
Sanarwar ta kuma bayyana cewa, jami’an hukumar tsaron farin kaya daga jamhuriyar Nijar ne suka biyo wanda ake zargin ɗan bindigar ne a kan babbar hanyar Zurmi/Kauran Namoda a jihar Zamfara.
Da yake duba makaman da aka kama, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana kyakkyawar haɗin gwiwa tsakanin sojojin da gwamnatin jihar Zamfara wajen yaƙi da ‘yan bindiga.
“Dole ne in yaba wa sojoji, DSS, da ‘yan sanda, musamman ma Hukumar Tsaro Ta Farin Kaya, bisa nasarar aiwatar da wannan gagarumin kame.
“Ina so in jaddada cewa waɗannan nasarori da aka samu tare da wasu na daƙile ‘yan bindiga a jihar, sun samo asali ne daga haɗin kai da goyon bayan da gwamnatin jihar Zamfara ke baiwa ɗaukacin jami’an tsaro.
“Za mu ci gaba da tallafa wa sojojin ta kowace hanya da za mu iya don ƙarfafa musu gwiwa su ci gaba da gudanar da ayyukansu.
“Zan yi farin ciki sanin cewa yawancin wafannan miyagun ‘yan asalin Zamfara ne. Ba baƙi ba ne, kuma wannan mutumin da aka kama ba shi kaɗai ba ne. Mun sami ire-iren waɗannan a cikin ’yan makonnin da suka gabata, amma wannan shi ne kaɗai muke gabatarwa ga jama’a. Irin wannan kamun na faruwa a kullum.
“’Yan bindiga na raguwa a Zamfara. Mun ga haka. Na buƙaci al’ummar Zamfara da su bai wa sojoji dukkan goyon bayan da suka dace.