‘Yan gwagwarmayar Siriya Sun Fara Kai Hare-Hare Kan Sojojin Mamayar Isra’ila
Published: 1st, February 2025 GMT
‘Yan gwagwarmayar Siriya sun sanar da fara kaddamar da hare-haren daukan fansa kan sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila
Sojojin mamayar Isra’ila sun yifuruci da cewa; Sun fuskanci bude wuta daga yankin kudancin Siriya, wanda kungiyar gwagwarmayar al’ummar Siriya ta yi ikirarin kai harin wanda shi ne irinsa na farko tun bayan da sojojin mamaya suka kutsa kai cikin yankunan Siriya bayan hambarar da gwamnatin tsohon shugaban kasar Siriya Bashar al-Assad.
Sojojin mamayar Isra’ila sun tabbatar da kai wani farmaki kan rundunar sojinsu a kudancin Siriya a jiya Juma’a.
A jiya ne sojojin mamayar Isra’ila suka kai farmaki kauyen Taranja da ke yankin Quneitra a kudu maso yammacin kasar Siriya, inda suka kame mutane biyu.
Wakilin gidan rediyon sojojin mamayar Isra’ila ya bayyana cewa: ‘Yan gwagwarmaya sun bude wuta kan sojojin mamayar Isra’ila a yankin Quneitra, yana mai cewa: Wannan shi ne karon farko da aka kai hari kan sojojin mamayar Isra’ila bayan watanni biyu suna yawo cikin ‘yanci a yankunan kasar Siriya.
Dan rahoton ya yi nuni da cewa: Ko wannan hari shi ne mafarin yunkurin ‘yan gwagwarmaya nuna rashin amincewarsu da matakan da sojojin mamayar Isra’ila suka dauka kan kasar Siriya na wuce gona da iri musamman ruguza duk wasu sansanonin soji da cibiyoyin binciken ilimin dabaraun yaki da wasu muhimman wuraren tsaro a kasar ta Siriya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: sojojin mamayar Isra ila kasar Siriya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Siriya Zata Samar Da Huldar Jakadanci Da HKI A Dai-Dai Lokacinda Ya Dace
Shugaban rikon kwarya na kasar Siriya Ahmed Al-sharaa ya bayyana cewa gwamnatinsa a shirye take ta samar da hulda da HKI a dai-dai lokacinda ya dace.
Jaridar Middle East Eye ta kasar Burtaniya ta nakalto Ahmed Sharaa yana fadar haka a wata wasikar da ya rubutawa shugaba Donal Trump
Har’ila yau shugaba Al-sharaa ya fadawa wani dan majalisar dokokin kasar Amurka kan cewa gwamnatinsa zata samar da huldar jakadanci da HKI a lokacinda ya dace, sannan a bangaren kasar Siriya kuma tana bukatar da farko a dagewa kasar takunkuman da aka dora mata, sannan yana son a yi maganar yankunan kasar Siriya wadanda HKI ta mamaye bayan juyin mulkin da aka yi a kasar.
Dan majalisar dokokin kasar ta Amurka Cory Mills na hannun daman Trump ya ziyarci kasar Siriya a makon da ya gabata inda ya gana da shugaban, na kimani minti 90, don tattaunawa wadannan al-amura
Mill dai wanda ziyarci kasar ta tare naukar nauyin yan kasar Siriya a Amurka ya bayyana kamfanin dillancin labaran Bloomberg kan cewa ya fadawa shugaban matakan da yakamata ya dauka don ganin an daukewa kasar takunkuman tattalin arziki.
Ya kuba bukaci shugaban wargaza sauran masana’antun makaman guba a kasar, ya shiga cikin kasashen yankin masu yaki da ayyukan ta’addanci, ya kuma san yadda zai yi da yan kasashen waje wadanda suke cikin HTS, wanda suka taimaka masa ya sami damar kifar da gwamnatin Bashar al-asad. Sannan dole ne ya amintar da HKI kan cewa ba zai kai mata hari ba.