HausaTv:
2025-03-07@18:09:10 GMT

‘Yan gwagwarmayar Siriya Sun Fara Kai Hare-Hare Kan Sojojin Mamayar Isra’ila

Published: 1st, February 2025 GMT

‘Yan gwagwarmayar Siriya sun sanar da fara kaddamar da hare-haren daukan fansa kan sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila

Sojojin mamayar Isra’ila sun yifuruci da cewa; Sun fuskanci bude wuta daga yankin kudancin Siriya, wanda kungiyar gwagwarmayar al’ummar Siriya ta yi ikirarin kai harin wanda shi ne irinsa na farko tun bayan da sojojin mamaya suka kutsa kai cikin yankunan Siriya bayan hambarar da gwamnatin tsohon shugaban kasar Siriya Bashar al-Assad.

Sojojin mamayar Isra’ila sun tabbatar da kai wani farmaki kan rundunar sojinsu a kudancin Siriya a jiya Juma’a.

A jiya ne sojojin mamayar Isra’ila suka kai farmaki kauyen Taranja da ke yankin Quneitra a kudu maso yammacin kasar Siriya, inda suka kame mutane biyu.

Wakilin gidan rediyon sojojin mamayar Isra’ila ya bayyana cewa: ‘Yan gwagwarmaya sun bude wuta kan sojojin mamayar Isra’ila a yankin Quneitra, yana mai cewa: Wannan shi ne karon farko da aka kai hari kan sojojin mamayar Isra’ila bayan watanni biyu suna yawo cikin ‘yanci a yankunan kasar Siriya.

Dan rahoton ya yi nuni da cewa: Ko wannan hari shi ne mafarin yunkurin ‘yan gwagwarmaya nuna rashin amincewarsu da matakan da sojojin mamayar Isra’ila suka dauka kan kasar Siriya na wuce gona da iri musamman ruguza duk wasu sansanonin soji da cibiyoyin binciken ilimin dabaraun yaki da wasu muhimman wuraren tsaro a kasar ta Siriya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin mamayar Isra ila kasar Siriya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 92, Sun Kubutar Da Mutane 75 A Cikin Mako Guda – DHQ

Maj.-Gen. Kangye ya kara da cewa dakarun da ke yaki da satar mai sun kwato lita 452,396 na danyen mai da aka sata, lita 224,175 na Man gas da aka tace ba bisa ka’ida ba, da kuma lita 1,920 na man fetur.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun hallaka mai haɗa wa Boko Haram bam a Sambisa
  • An Kashe Mutum Akalla 70 A Yaki Tsakanin HKS Da Yan Tawaye A Kudancin Kasar Siriya
  • Kasar Chaina Ta Yi Gargadin Cewa Duniyar Zata Zama Ba Doka Da Oda Idan Amurka Ta Ci Gaba Da Yakin Kudaden Fito Da Ta fara
  • MDD Ta Nuna Damuwarta Da Abinda ke Faruwa A Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • An Ayyana Dokar Ta-baci A Wasu Yankunan Siriya
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 92, Sun Kubutar Da Mutane 75 A Cikin Mako Guda – DHQ
  • Ayukkan Sojoji Na Taimakawa Wajen Samar da Tsaro a Taraba
  • Wata Kotu A Iran Ta Ci Taran  Gwamnatin Amurka Dala Biliyon $12.6 Saboda Haddasa Mutuwar Masu Fama Da Cutar ‘thalassemia’ A Kasar
  • Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ta Amince Da Gazawarta Wajen Hana Harin Hamas
  • Gaza : Afirka Ta Kudu Ta Zargi Isra’ila Da Amfani Da Yunwa A Matsayin Makamin Yaki