HausaTv:
2025-04-07@08:01:46 GMT

‘Yan gwagwarmayar Siriya Sun Fara Kai Hare-Hare Kan Sojojin Mamayar Isra’ila

Published: 1st, February 2025 GMT

‘Yan gwagwarmayar Siriya sun sanar da fara kaddamar da hare-haren daukan fansa kan sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila

Sojojin mamayar Isra’ila sun yifuruci da cewa; Sun fuskanci bude wuta daga yankin kudancin Siriya, wanda kungiyar gwagwarmayar al’ummar Siriya ta yi ikirarin kai harin wanda shi ne irinsa na farko tun bayan da sojojin mamaya suka kutsa kai cikin yankunan Siriya bayan hambarar da gwamnatin tsohon shugaban kasar Siriya Bashar al-Assad.

Sojojin mamayar Isra’ila sun tabbatar da kai wani farmaki kan rundunar sojinsu a kudancin Siriya a jiya Juma’a.

A jiya ne sojojin mamayar Isra’ila suka kai farmaki kauyen Taranja da ke yankin Quneitra a kudu maso yammacin kasar Siriya, inda suka kame mutane biyu.

Wakilin gidan rediyon sojojin mamayar Isra’ila ya bayyana cewa: ‘Yan gwagwarmaya sun bude wuta kan sojojin mamayar Isra’ila a yankin Quneitra, yana mai cewa: Wannan shi ne karon farko da aka kai hari kan sojojin mamayar Isra’ila bayan watanni biyu suna yawo cikin ‘yanci a yankunan kasar Siriya.

Dan rahoton ya yi nuni da cewa: Ko wannan hari shi ne mafarin yunkurin ‘yan gwagwarmaya nuna rashin amincewarsu da matakan da sojojin mamayar Isra’ila suka dauka kan kasar Siriya na wuce gona da iri musamman ruguza duk wasu sansanonin soji da cibiyoyin binciken ilimin dabaraun yaki da wasu muhimman wuraren tsaro a kasar ta Siriya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin mamayar Isra ila kasar Siriya

এছাড়াও পড়ুন:

Fedpoly Bauchi Ta Sanya Na’urorin Ɗaukan Hoto ‘CCTV’ Don Daƙile Satar Jarabawa Da Inganta Tsaro

Da ya ke magana kan ziyarar tawatar NBTE, Rector ɗin ya ce aikin sahalewa na da matuƙar muhimmanci domin gano irin ƙoƙari da azamar makaranta a cikin shekaru biyar da suka gabata da nufin tabbatar kayan koya da koyarwa da malamai suna nan kan tsarin da aka amince da tafiyar da su tun da farko.

Ya tabbatar da cewa kwasa-kwasai har guda 78 ne jami’an NBTE suka nazarta a yayin wannan ziyararz, “Tawagar sun gama aikin su na ziyarar, yanzu haka muna zaman jiran sakamakon bincike da bin sawun nasu ne,” ya ƙara shaida.

A nata ɓangaren, Dakta Fatima Umar, daraktan shirye-shiryen kwalejoji kuma jagorar tawagar na NBTE, ta buƙaci kwalejin Kimiyya da fasaha na gwamantin tarayya da ke Bauchi da ya maida hankali wajen magance matsalolin gine-gine da kuma giɓin ma’aikata.

Da take samun wakilcin Adesina Oluade, ta jero sauran matsalolin da ta gano kamar ƙarancin littafai na ɗalibi, mujallu na ilimi, rashin samar da wutar lantarki yadda ya kamata, inda ta ce bangarorin na buƙatar daukan matakan gaggawa.

Umar ta jaddada cewa tsarin sahalewa na da nufin ƙarfafa tabbatar da samar da ilimi mai ingancin da kyautata aiki, inda ta sha alwashin cewa kwamitin zai cigaba da yin gaskiya da adalci a yayin aikinsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hassan Fadlallah: Amurka ke da alhakin ayyukan wuce gona da iri na Isr’aila a Lebanon
  • Rahoto: Yara Falasdinawa 350 ne Isra’ila ke tsare da su a gidajen kurkuku
  • Fedpoly Bauchi Ta Sanya Na’urorin Ɗaukan Hoto ‘CCTV’ Don Daƙile Satar Jarabawa Da Inganta Tsaro
  • Trump Ya Yada Hutunan Bidiyo Wadanda Suka Nuna Yadda Sojojin Amurka Suka Kashe Mutanen Yemen Wadanda Suke Bukukuwan Salla Karama
  • Faifan bidiyo ya fallasa kisan gillar da Isra’ila ta yi wa likitoci  a Gaza
  • Burtaniya Ta Soki Gwamnatin Netanyahu Kan Hana ‘Yan Majalisarta Biyu Shiga Cikin Isra’ila
  • Red Crescent ta Falasdinu ta nemi a yi bincike kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji
  • Sudan: Ana Ci Gaba Da Yin Fada Tsakanin Sojoji Da Rundunar Daukin Gaggawa A Um-Durman
  • Al-Houthi: Hare-haren Amurka sun kasa dakatar da gwagwarmayar Yeman
  • Wani Kusa A Kungiyar Hamas Ya Yi Shahada A Wani Harin Isra’ila A Kudancin Lebanon