Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kaddamar Da Wasu Sabbin Makamai Masu Linzami
Published: 1st, February 2025 GMT
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun kaddamar da sabbin na’urori masu linzami da na tsaro
Babban sakataren rundunar da ke sa ido kan dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya sanar da kaddamar da wasu sabbin na’urori masu linzami da na tsaro a cikin tsarin baje kolin “Malik Ashtar”, wanda za a gudanar a ranar Litinin mai zuwa a kasar.
Birgediya Janar Hamid Bazmashahi ya kara da cewa a wani taron manema labarai a yau Asabar, za su yaye shamakin makaman dakarun kare juyin juya halin Musulunci na kare karfinsu bisa tsarin baje kolin.
Ya yi nuni da cewa, baje kolin zai hada da, a karon farko, baje kolin jami’an tsaron da ke sintiri da jiragen ruwa masu dauke da aluminium, baya ga nasarorin da aka samu a fannin fasahar kere-kere da Karin adadi makamai.
Ya kara da cewa yana ganin dakarun kare juyin juya halin Musulunci a matsayin wata cibiya da ke da ayyuka da yawa a matakin duniya baki daya, kuma baje kolin zai tattauna wani bangare na ayyukan dakarun kare juyin juya halin da kuma yada shi ga kafafen watsa labarai.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin juya halin Musulunci
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta Bukaci Falasdinawa A Birnin Qudus Su Sabawa Dokar Takaita Yawan Masu Shiga Masallacin Al-Aksa A Kudus
Wata kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ta bada rahoton cewa sojojin HKI sun kashe akalla yara 16 tun farkon wannan shekara ta 2025 a yankin yamma da kogin Jordan.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Ayed Abu Eqtaish, daraktan kungiyar ‘ The Defense for Children International’ a yankin yamma da kogin Jordan yana fadar haka. Ya kuma zargi manya manyan kasashen duniya da kyale gwamnatin HKI tana aikata irin wadannan laifuka kan Falasdinawa a gaban idan kowa.
Eqtaish ya kara da cewa, rashin magana da kuma takawa gwamnatin yahudawan birki yana sa ta kara yawan kashe yara Falasdinawa a duk sanda ta ga dama.
Kafin haka wani rahoton MDDya bayyana cewa idan ba’a hana HKI da karfi ba, to ba za ta takaita kisan kiyanshi a Gaza kadai ba, zata fadadashi zuwa yankin yamma da kogin Jordan.
Sojojin HKI sun ta aikata kissan kiyashi a gaza a yain fin karfin da ta yi a Gaza na tsawon watanni 15, inda ta kashe fal;asdinawa fiye da 61,000 kafin a tsagaita wuta a ranar 19 ga watan Jenerun da ya gabata.