Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kaddamar Da Wasu Sabbin Makamai Masu Linzami
Published: 1st, February 2025 GMT
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun kaddamar da sabbin na’urori masu linzami da na tsaro
Babban sakataren rundunar da ke sa ido kan dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya sanar da kaddamar da wasu sabbin na’urori masu linzami da na tsaro a cikin tsarin baje kolin “Malik Ashtar”, wanda za a gudanar a ranar Litinin mai zuwa a kasar.
Birgediya Janar Hamid Bazmashahi ya kara da cewa a wani taron manema labarai a yau Asabar, za su yaye shamakin makaman dakarun kare juyin juya halin Musulunci na kare karfinsu bisa tsarin baje kolin.
Ya yi nuni da cewa, baje kolin zai hada da, a karon farko, baje kolin jami’an tsaron da ke sintiri da jiragen ruwa masu dauke da aluminium, baya ga nasarorin da aka samu a fannin fasahar kere-kere da Karin adadi makamai.
Ya kara da cewa yana ganin dakarun kare juyin juya halin Musulunci a matsayin wata cibiya da ke da ayyuka da yawa a matakin duniya baki daya, kuma baje kolin zai tattauna wani bangare na ayyukan dakarun kare juyin juya halin da kuma yada shi ga kafafen watsa labarai.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin juya halin Musulunci
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Jinjinawa ‘Yan Najeriya Mazauna Kasashen Waje Bisa Nuna Halin Dattaku
Shugaba Bola Tinubu ya bayyana farin cikinsa bisa rahotanin da ya samu game kyawawan dabi’u da ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje suke nunawa a kasashen da suke, yana mai cewa hakan zai zaburar da matasa kan dabi’un da ke kara martabar kasa.
Shugaban ya yabawa ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje yayin da ya karbi wasiku daga jakadan kasar Kanada a Najeriya, Pasquale Salvaggio, da jakadan Saliyo, Dr Julius F. Sandy, a fadar gwamnati.
Har ila yau, shugaba Tinubu ya karbi wasikun amincewa da nuna gamsuwa daga Legesse Geremew Haile, jakadan kasar Habasha a Najeriya, da Archbishop Michael Francis Crotty, shugaban Bishop Bishop na fadar Vatican a Najeriya.
Babban Kwamishinan na Kanada ya shaida wa Shugaba Tinubu cewa ’yan Najeriya suna da himma a fannin ilimi, da wasannin motsa jiki, da kimiyya, da lafiya, da kasuwanci a kasarsa.
Ya ce ‘yan Najeriya a Kanada suna nuna kyawawan dabi’u da wayewa, da kwazo yayin cimma burinsu.
Salvaggio, wanda a baya ya yi aiki a Ghana da Cote’Ivoire, ya ce Kanada na neman fadada sha’awarta a kan man fetur da iskar gas, da al’amuran da suka shafi fasahar zamani, da noma, a dangantakar ta Najeriya.
Shugaba Tinubu ya yaba da nasarorin da ‘yan Najeriya suka samu a kasashen waje, yana mai bayyana su a matsayin abin zaburarwa ga mutane da dama.
A wani taron da ya yi da babban jakadan Saliyo kuwa, shugaba Tinubu ya tabbatar da cewa, muradin Najeriya na ci gaban gabar tekun Yamma da Afirka shi ne abin da ya sa a gaba.
Shugaban ya shaida wa jakadan cewa jarin da Najeriya ta yi a Saliyo na tsawon shekaru da dama ya taimaka wajen ci gaban Afirka da kuma inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.
Jakadan ya godewa shugaban kasar bisa goyon bayan da Najeriya ke bayarwa wajen cigaban kasarsa.
Ya ce “A Saliyo, ‘yan Najeriya sun fi ‘yan kasar yin kasuwanci, yawancin malamai a makarantu ‘yan Najeriya ne, babu bambanci tsakanin dan Najeriya da dan Saliyo idan kana tafiya a kan titin Freetown.”
“Muna bukatar ci gaba da neman zaman lafiya a nahiyarmu, ya kamata mu hada karfi da karfe wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, kalubalen da muke fuskanta a Afirka shi ne rashin tsaro, wanda ke hana ci gaba, ba mu da wanda zai kawo mana zaman lafiya, ssai in mun yi aiki tukuru.” in ji shi.
Daga Bello Wakili