Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kaddamar Da Wasu Sabbin Makamai Masu Linzami
Published: 1st, February 2025 GMT
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun kaddamar da sabbin na’urori masu linzami da na tsaro
Babban sakataren rundunar da ke sa ido kan dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya sanar da kaddamar da wasu sabbin na’urori masu linzami da na tsaro a cikin tsarin baje kolin “Malik Ashtar”, wanda za a gudanar a ranar Litinin mai zuwa a kasar.
Birgediya Janar Hamid Bazmashahi ya kara da cewa a wani taron manema labarai a yau Asabar, za su yaye shamakin makaman dakarun kare juyin juya halin Musulunci na kare karfinsu bisa tsarin baje kolin.
Ya yi nuni da cewa, baje kolin zai hada da, a karon farko, baje kolin jami’an tsaron da ke sintiri da jiragen ruwa masu dauke da aluminium, baya ga nasarorin da aka samu a fannin fasahar kere-kere da Karin adadi makamai.
Ya kara da cewa yana ganin dakarun kare juyin juya halin Musulunci a matsayin wata cibiya da ke da ayyuka da yawa a matakin duniya baki daya, kuma baje kolin zai tattauna wani bangare na ayyukan dakarun kare juyin juya halin da kuma yada shi ga kafafen watsa labarai.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin juya halin Musulunci
এছাড়াও পড়ুন:
Iran za ta karbi bakuncin taron farko kan kare hakkin dan Adam a Gabas ta tsakiya
Jamhuriyar Musulinci ta Iran, za ta karbi bakuncin taron farko na kasa da kasa kan kare hakkin bil adama a Gabas ta Tsakiya.
Shugaban Hukumar Al’adu da Sadarwa ta Musulunci Mohammad Mehdi Imanipour ya bayyana cewa, za a gudanar da taron farko na kasa da kasa kan batun kare hakkin bil’adama kan Gabas ta Tsakiya a lokaci guda a Tehran, Qom da Isfahan daga ranar 28 ga Afrilu zuwa 2 ga Mayu.
Hakkin dan adam na daya daga cikin batutuwan da suka fi muhimmanci a cikin al’ummomi, saidai a baya bayan nan wasu gwamnatoci sun yi watsi da yancin dan adam gaba daya.
Mohammad Mehdi Imanipour ya ce “A yau, misali karara na take hakkin bil’adama shi ne kisan kiyashi da ake yi a Gaza.”
Ya ce Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da abubuwa da dama da za ta iya fada a fagen kare hakkin bil’adama, don haka ta kai ga gayyatar wasu kasashe a wannan taro domin neman kafa kawancen kare hakkin bil’adama na duniya mai sabon salo.
An aika gayyata a hukumance ga kasashem duniya 32 da kuma manyan cibiyoyin kimiyya da ilimi 36 dake hadin gwiwa tare da taron.