Ci Gaban Tsaro Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Yana Sanya Makiya Iran Takaici
Published: 1st, February 2025 GMT
Babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran ya bayyana cewa; Abubuwan da suka nuna irin girman dakarun kare juyin juya halin Musulunci sun sanya makiya takaici
Babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Manjo Janar Mohammad Baqiri ya jaddada cewa bayyanar irin girman da dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran suke da shi ya sanya makiya takaici.
Hakan ya zo ne a daidai lokacin da Manjo Janar Baqiri ya aike da sakon murna ga kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci, Manjo Janar Hossein Salami, a yau Asabar, dangane da bukukuwan watan Sha’aban, ciki har da zagayowar ranar haihuwar Imam Husaini (a.s), wanda ya zo daidai da ranar dakarun kare juyin juya halin Musulunci.
Yana mai jaddada cewa; Yana da imanin cewa dakarun kare juyin juya halin Musulunci suna bayyana ne ga kowane dan kasar Iran a cikin wani yanayi mai girma a fagen gwagwarmayar Musulunci a wannan yanki, kuma hakan yana sanya al’ummar musulmi alfahari.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin juya halin Musulunci
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Jaddada Matsayinta Kan Batun Tace Sinadarin Yuranium A Batun Tattaunawa Da Amurka
Jamuhuriyar Musulunci ta Iran ta jaddada matsayinta kan batun tace sinadarin yuraniyo.
Mai magana da yawun gwamnatin Iran Fatemeh Mohajerani ta bayyana cewa, Iran na kokarin yin shawarwari ne domin samar da amana da samar da gaskiya game da shirinta na nukiliya domin dage takunkumi kanta.
A cikin taron manema labarai na mako-mako da ta gudanar a jiya litinin, Mohajerani ta mayar da martani ga wata tambaya game da tattaunawar da ake yi tsakanin Iran da Amurka, inda ta ce, shin bangarorin biyu sun cimma matsaya dangane da kasar da za a aike da hajojin uranium da Iran ta inganta? Shin Iran ta amince ta mika wadannan haja zuwa Rasha? Ta ce: Ina so in bayyana dangane da kashi na farko na tambayar cewa wasu daga cikin wadannan lamurra jajayen layukan Iran ne.
Wasu batutuwa a bude suke don tattaunawa, amma, kamar yadda aka ambata a baya, wasu daga cikin abubuwan da ake tattaunawa a kafafen yada labarai sun fada cikin jajayen layin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ne, dangane da kasar Rasha, tana jaddada cewa, a matsayinta na mamba na dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya tana da matukar muhimmanci a wurin Iran, kuma hadin gwiwar kut-da-kut da ke tsakanin Iran da Rasha, ya bai wa kasar Rasha rawar da ta taka wajen yin shawarwarin.