Matasa 150 Sun Halarci Gasar Kirkire-Kirkiren Fasaha a Kano
Published: 1st, February 2025 GMT
Aƙalla matasa 150 masu kirkire-kirkire daga yankin Arewa sun hallara a Kano don halartar “Innovate North” Business Development and Innovation Hackathon, wani shiri da ke da nufin ƙarfafa harkokin kasuwanci da sauya fasalin dijital.
Yayin da take jawabi a taron, Maryam Lawan Gwadabe, wacce ta shirya gasar kuma ita ce wanda ta kafa Blue Sapphire Hub, ta jaddada mahimmancin shiryawa da ba da jagora ga matasa domin bunkasa basirarsu.
“Yawancin matasa masu kirkire-kirkire ba su da jagora ko kuma wanda zai taimaka musu su sauya tunaninsu zuwa kasuwanci mai ɗorewa,” in ji ta.
Gwadabe ta bayyana gasar a matsayin babbar dama da ke bai wa matasa ‘yan Najeriya zarafin nuna fasaharsu a fannin kimiyya, fasaha da kirkire-kirkire.
Gasar ta ƙunshi kungiyoyi 30 — kowacce tana da mutum biyar, inda suka nuna basirarsu a bangaren dijital da kasuwanci a cikin yanayi na gasa.
Da yake wakiltar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, Kwamishinan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire, Yusuf Kofar Mata, ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar na da cikakken shirin tallafa wa matasa a fannin kirkire-kirkire da fasahohin zamani.
Ya bayyana cewa gwamnati na da shirin horar da mutum miliyan ɗaya a fannin fasahar sadarwa ta ICT kafin ƙarshen wa’adin mulkinsu.
“Abin alfahari ne ganin matasa maza da mata suna bada gudunmawa a fannin kirkire-kirkire na zamani.
“Gwamnatin Jihar Kano za ta ci gaba da tallafa musu, kuma Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf na da shirin ciyar da wannan fanni gaba cikin shekara guda,” in ji Kofar Mata.
Ya kuma jaddada cewa fasahohin zamani na da gagarumin tasiri a tattalin arziki, inda ya buƙaci matasa su yi amfani da fasaha ta hanyoyin da za su amfane su, tare da cin moriyar damar da ke cikin ɓangaren ICT.
“Kafin ƙarshen wannan wa’adin mulki, muna da shirin horar da mutum miliyan ɗaya da fasahar dijital, domin su sami abin dogaro da kansu tare da bada gudunmawa wajen ci gaban Kano da Najeriya gaba ɗaya,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa Jihar Kano Maryam Gwadabe
এছাড়াও পড়ুন:
Fulham ta doke Liverpool bayan wasa 26 a jere ba tare da rashin nasara ba
Fulham ta kawo ƙarshen wasanni 26 da Liverpool ta yi a jere ba tare da rashin nasara ba a gasar Firimiyar Ingila ta wannan kakar.
Fulham ta yi nasarar doke Liverpool da 3-2 a Craven Cottage ranar Lahadi a wasan mako na 31.
Liverpool ce ta fara zura ƙwallo a ragar Fulham ta hannun Mac Allister minti 14 da fara wasa kafin Ryan Sessegnon ya rama wa Fulham a minti 23.
Fulham ba ta yi ƙasa a gwiwa ba sai da ta ƙara wa Liverpool ƙwallo ɗaya a lokacin da ɗan wasan Nijeriya, Alex Iwobi ya zura ƙwallo a ragar Liverpool a minti 32 da fara wasa.
Yayin da ake tunanin cewa Liverpool za ta iya ramawa, sai Fullham ta ƙara mata ƙwallo na uku a lokacin da Rodrigo Muniz ya zura ƙwallo a ragar Liverpool minti 37 da fara wasa.
An dai tafi hutun rabin lokaci Fullham na da rinjaye a kan Liverpool da ci 3-1 yayin da ake tunanin cewa komai na iya faruwa idan aka dawo daga hutun.
Bayan an dawo daga hutun rabin lokaci, Liverpool ta yi ta ƙoƙarin ɗaukar fansa domin ta samu ko da maki ɗaya ne daga wasan, sai dai haƙarta bai cim ma ruwa ba har sai minti 72 da fara wasa.
A minti 72 da fara wasan ne Luiz Diaz ya zura ƙwallo ɗaya a ragar Fullham lamarin da ya mayar da wasan 3-2.
Sai dai kuma Liverpool ba ta iya ƙara wa Fulham ba domin Fulham ta samu ta kare rinjayenta a wasan kuma ta cinye maki ukun wasan gaba ɗaya.
Duk da wannan sakamako, Liverpool ce ke ci gaba da jan ragama a saman teburin gasar Firimiya da maki 73 duk da cewa ba ta ƙara ratar da ta bai wa Arsenal da ke biye da ita ba.
Ita kuwa Fulham tana ta takwas a teburin gasar Firimiya inda take da maki 48.
Kociyan Liverpool, Arne Slot wanda ya ce kungiyarsa ta cancanci wannan sakamako, ya tabbatar da cewa ’yan wasansa sun tafka kura-kurai da ya zama tilas su dauki izina a kai.