Aminiya:
2025-03-04@03:28:23 GMT

Matasa 150 Sun Halarci Gasar Kirkire-Kirkiren Fasaha a Kano

Published: 1st, February 2025 GMT

Aƙalla matasa 150 masu kirkire-kirkire daga yankin Arewa sun hallara a Kano don halartar “Innovate North” Business Development and Innovation Hackathon, wani shiri da ke da nufin ƙarfafa harkokin kasuwanci da sauya fasalin dijital.

Yayin da take jawabi a taron, Maryam Lawan Gwadabe, wacce ta shirya gasar kuma ita ce wanda ta kafa Blue Sapphire Hub, ta jaddada mahimmancin shiryawa da ba da jagora ga matasa domin bunkasa basirarsu.

APC ta kori tsohon Gwamnan Osun, Aregbesola daga jam’iyyar Yadda Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass ya yi wa Tinubu addu’ar nasara

“Yawancin matasa masu kirkire-kirkire ba su da jagora ko kuma wanda zai taimaka musu su sauya tunaninsu zuwa kasuwanci mai ɗorewa,” in ji ta.

Gwadabe ta bayyana gasar a matsayin babbar dama da ke bai wa matasa ‘yan Najeriya zarafin nuna fasaharsu a fannin kimiyya, fasaha da kirkire-kirkire.

Gasar ta ƙunshi kungiyoyi 30 — kowacce tana da mutum biyar, inda suka nuna basirarsu a bangaren dijital da kasuwanci a cikin yanayi na gasa.

Da yake wakiltar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, Kwamishinan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire, Yusuf Kofar Mata, ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar na da cikakken shirin tallafa wa matasa a fannin kirkire-kirkire da fasahohin zamani.

Ya bayyana cewa gwamnati na da shirin horar da mutum miliyan ɗaya a fannin fasahar sadarwa ta ICT kafin ƙarshen wa’adin mulkinsu.

“Abin alfahari ne ganin matasa maza da mata suna bada gudunmawa a fannin kirkire-kirkire na zamani.

“Gwamnatin Jihar Kano za ta ci gaba da tallafa musu, kuma Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf na da shirin ciyar da wannan fanni gaba cikin shekara guda,” in ji Kofar Mata.

Ya kuma jaddada cewa fasahohin zamani na da gagarumin tasiri a tattalin arziki, inda ya buƙaci matasa su yi amfani da fasaha ta hanyoyin da za su amfane su, tare da cin moriyar damar da ke cikin ɓangaren ICT.

“Kafin ƙarshen wannan wa’adin mulki, muna da shirin horar da mutum miliyan ɗaya da fasahar dijital, domin su sami abin dogaro da kansu tare da bada gudunmawa wajen ci gaban Kano da Najeriya gaba ɗaya,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Jihar Kano Maryam Gwadabe

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki domin tallafa wa mabuƙata a wannan wata mai albarka na Ramadana.

Mataimakin Gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ne ya ƙaddamar da rabon abincin a cibiyar Dandali da ke Ƙaramar Hukumar Fagge a jihar.

HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja NLC ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki

Bayanai sun ce gwamnatin jam’iyyar NNPP ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf da ta ƙaddamar da wannan shiri tana da burin raba abincin buɗa-baki ga mabuƙata masu azumtar watan Ramadana.

Gwamnatin ta ce an tanadi cibiyoyi 91 domin raba wa mabuƙata 91,000 abincin buɗa-baki duk rana nan da tsawon kwanaki 27 masu zuwa.

Domin tabbatar da samun nasara, gwamnatin ta ce ta ɗauki masu aikin girke-girke da za su riƙa dafawa sannan su raba wa mabuƙata abincin.

Mataimakin Gwamnan wanda shi ne ke jagorantar shirin raba abincin a bana, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka ƙaddamar da shirin, yana mai kiran waɗanda aka ɗora wa alhakin aikin su tabbatar da raba wa mabuƙata abincin a kan kari.

Aminiya ta ruwaito cewa, Mataimakin Gwamnan ya samu rakiyar wasu ƙusoshin Gwamnatin Kano wajen ƙaddamar da rabon abincin da suka haɗa da Kwamishinan Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya da Kwamishinan Harkokin Addini, Sheikh Tijjani Auwal da sauransu.

Gwamnatin Kano ta jaddada ƙudirinta na rage raɗaɗin al’umma musamman Musulmi a wannan wata mai falala.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masar : Za’a Gabatar Da Shirin Baiwa Falasdinawa Yancin Zama A Kasarsu
  • Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar Da Shirin Ciyarwar Na Watan Ramadan
  • Masar Za Ta Bayyana Shirin Sake Gina Gaza A Yayin Taron Larabawa
  • Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano
  • An kama ɓarayin waya a Kano
  • Shin Liverpool Za Ta Kai Labari Ba Tare Da Muhammad Salah Ba?
  • Iran Ta Zama Zakara A Damben Gargajiya Ta 2025 UWW Wanda Aka Gudanar A Kasar Albaniya
  • Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno
  • Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250