Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun kaddamar da sabbin na’urori masu linzami da na tsaro

Babban sakataren rundunar da ke sa ido kan dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya sanar da kaddamar da wasu sabbin na’urori masu linzami da na tsaro a cikin tsarin baje kolin “Malik Ashtar”, wanda za a gudanar a ranar Litinin mai zuwa a kasar.

Birgediya Janar Hamid Bazmashahi ya kara da cewa a wani taron manema labarai a yau Asabar, za su yaye shamakin makaman dakarun kare juyin juya halin Musulunci na kare karfinsu bisa tsarin baje kolin.

Ya yi nuni da cewa, baje kolin zai hada da, a karon farko, baje kolin jami’an tsaron da ke sintiri da jiragen ruwa masu dauke da aluminium, baya ga nasarorin da aka samu a fannin fasahar kere-kere da Karin adadi makamai.

Ya kara da cewa yana ganin dakarun kare juyin juya halin Musulunci a matsayin wata cibiya da ke da ayyuka da yawa a matakin duniya baki daya, kuma baje kolin zai tattauna wani bangare na ayyukan dakarun kare juyin juya halin da kuma yada shi ga kafafen watsa labarai.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin juya halin Musulunci

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Sansanin Nevatim Na Harahtacciyar Kasar Isra’ila Da Makami Mai Linzami

Sojojin Yemen sun kai hari kan sansanin Nevatim na haramtacciyar kasar Isra’ila da ke Negev da makami mai linzami

Dakarun Yemen sun sanar da aiwatar da wani farmakin soji kan sansanin sojojin saman Nevatim na haramtacciyar kasar Isra’ila da ke yankin Negev a kudancin Falasdinu da aka mamaye.

Rundunar sojin kasar Yemen ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Asabar cewa: Rundunarta ta kai wani harin soji kan sansanin sojin saman Nevatim da ke yankin Negev da makami mai linzami na kirar  “Falestine 2”.

Majiyar ta kara da cewa: Makami mai linzamin ya kai ga inda aka saita, kuma na’urorin kariya na haramtacciyar kasar Isra’ila sun kasa kakkaboshi. Ta yi nuni da cewa: Wannan farmakin wata nasara ce ga al’ummar Falastinu da ake zalunta da mayakansu, da kuma yin watsi da kisan kiyashin da makiya yahudawan sahayoniyya suke yi kan ‘yan uwan al’ummar Yemen a Zirin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Sarkin Daura Zai Karrama Ja’o’ji Da Wasu Samarin Arewa
  • Kungiya Ta Bai Wa Marayu Tallafin Atamfofi Da Shaddodi A Yobe 
  •  Dakarun Kai Daukin Gaggawa Na Sudan Sun kashe ‘Yan Hijira Da Dama A Yankin Tekun Maliya
  • Iran ta Bayyana cewa: TattaunawarMuscat Wata Dama Ce Ta Samun Zaman Lafiya Kan Batutuwan Masu Sarkakiya
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Sansanin Nevatim Na Harahtacciyar Kasar Isra’ila Da Makami Mai Linzami
  • Wang Yi Ya Ce Kasar Sin Za Ta Magance Cin Zarafin Da Amurka Ke Yi Ita Kadai