Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera
Published: 1st, February 2025 GMT
Ga Yadda Za Ku Yi.
Da farko dai za ki tanadi AloeBeranki wanda ya rika, sai ki wanke shi, ki dare shi don cire wannan yaukin da ke cikinsa ki saka shi a roba Mai tsafta. Bayan kin saka a roba ko kwano,sai ki samo blender, ki markada shi, idan ya markadu ya na dawowa fari, sai ki zuba a kwano.
Sannan ki samu Sabulun base din ki ana sayar da shi a shagon sayar da chemicals, da kin ce kina son Sabulun base za su ba ki.
Ki kunna gas din ki ko gawayi sai ki dora ruwa a tukunya ki sa ruwan daidai yadda idan kika saka kwanon silber din da kika sawa Sabulun base zai shiga.
Idan ruwan ya yi zafi sai ki saka kwanon silber din cikin tukunyan kamar turarawa kenan, sai ki yi ta juya Sabulun zai narke, idan ya narke, sai ki sauke ki saka markadadden Aloe Beran ki ciki.
Idan kin saka ki juya ki dauko bitamin E Capsule din ki, za ki iya samun shi a chemist idan kika ce kina son bitamin E Capsule za a baki sai ki yanka shi sai ki saka ruwan cikin hadin ki, ki kawo Kala ko food colour ki saka a ciki don ya ba da kalar Aloe Bera, ki jujjuya hadin har sai sun hadu
Sai kuma ki samo roba wacce za ta ba ki shape din da kike so, ki goge da mai don Sabulun ya fita da sauki.
Ki shafa Mai a robar, ko ta Ice cream ce sai ki zuba hadinki cikin robar, amma kar ki zuba ta a lokacin da take da zafi sosai saboda kar ta kone miki roba, sai ki bar ta ta sha iska za ki iya barin ta ta kwana daya ko ta wuni.
Daga nan sai ki cire ki mata packaging Mai kyau. Shi Kenan Sabulun ki ta yi hadu sai sayarwa.
Za ki iya tallata abinki a kafofin sada zumuntar zamani (Social media)
এছাড়াও পড়ুন:
Dan jarida Ahmad Mansour ya yi shahada bayan sojojin Isra’ila sun kona shi da ransa a Gaza
A safiyar jiya litinin an kashe wani dan jarida Bafalasdine da wani matashi tare da raunata wasu da dama a lokacin da jirgin Isra’ila ya kai hari kan wani tanti na ‘yan jarida a kusa da rukunin likitocin Nasser da ke Khan Younis a kudancin Gaza.
Wakilin Al Mayadeen ya ruwaito cewa dan jarida Hilmi al-Faqawi da wani matashi mai suna Yousef al-Khazindar sun yi shahada, yayin da wasu ‘yan jarida da suka hada da Ahmed Mansour, Hassan Islayh, Ahmed al-Agha, Mohammed Fayek, Abdullah al-Attar, Ihab al-Bardini, Mahmoud Awad, da Majed Qudaih, suka samu raunuka a tashin bam din.
Kungiyar Kafafen Yada Labarai ta Falasdinu ta yi Allah wadai da wannan harin da Isra’ila ta kai a kan tantin ‘yan jarida a Khan Yunus, tare da nuna alhinin rasuwar dan jarida Hilmi al-Faqawi, wakilin tashar talabijin ta Falasdinu Alyaum.
Kisan dan jarida Ahmad Mansour ya janyo tofin Allah tsine daga kasashen Larabawa da ma duniya baki daya.
Kwamitin kasa da kasa da ke goyon bayan hakkin al’ummar Palasdinu ya yi tir da harin, inda ya bayyana shi a matsayin laifin yaki da nufin rufe bakin ‘yan jaridu tare da dakile bayanan cin zarafin da Isra’ila ke yi a Gaza.
Masu fafutuka na kafofin watsa labarun sun kuma nuna rashin jin dadi, suna nuna yadda Isra’ila ke ci gaba da cin zarafin ɗan adam-musamman a kan ‘yan jarida, waɗdanda ke da hakkin samun kariya a karkashin dokar jin kai ta duniya. A cewar ofishin yada labarai na gwamnati a Gaza, adadin ‘yan jaridar da aka kashe tun ranar 7 ga watan Oktoba 2023 ya zarce 210.