An miƙa wa Majalisar Kano ƙorafin ƙara wa’adin manyan ma’aikatan gwamnati
Published: 1st, February 2025 GMT
An miƙa wa Majalisar Dokokin Kano ƙorafi kan abin da aka bayyana a matsayin ƙarin wa’adin aiki na wasu manyan jami’an gwamnati ba bisa ƙa’ida ba.
A ƙunshin ƙorafin an yi zargin cewa ana ƙara wa manyan jami’an wa’adin aiki ta hanyar amfani da Dokar Zartarwa Ta 1 ta 2025, wadda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanyawa hannu.
A cikin wata wasika mai kwanan wata 6 ga Janairu, 2025, Sani Usman DanAbdullo, Esq., Daraktan Gudanarwa da Harkokin Gabaɗaya na Hukumar Yaki da Cutar Kanjamau ta Jihar Kano (KSACA), ya buƙaci Majalisa da ta kare doka da oda, tare da dakatar da abin da ya bayyana a matsayin rashin amfani da ikon zartarwa yadda ya kamata.
An aike da ƙorafin ne zuwa ga Kakakin Majalisar, Hon. Jibrin Ismail Falgore, da kuma Shugaban Kwamitin Majalisa kan Ƙorafe-ƙorafe na Jama’a.
Takardar ta ƙalubalanci Dokar Zartarwa da aka fitar a ranar 1 ga Janairu, 2025, wadda ake zargi da bayar da ƙarin shekaru biyu ga Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, Magatakardan Majalisa, wasu alƙalai, da ma’aikatan ɓangaren lafiya.
Ana iya tuna cewa Gwamna Yusuf ya amince da ƙarin wa’adin shekaru biyu ga Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, wasu Manyan Sakatarori, da manyan ma’aikatan gwamnati, wanda zai fara aiki daga 31 ga Disamba, 2024.
Gwamnan ya kare wannan mataki, yana mai cewa Dokar Buƙatar Dole (Doctrine of Necessity) ce ta tilasta hakan, yana mai dogaro da sassa 5(2) da 208 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999.
Sai dai a cikin ƙorafin, an bayyana cewa wannan umarni ya ci karo da dokokin jihar, musamman Dokar Fansho da Giratuti ta Jihar Kano (Gyara Na 5), 2024, wadda ta tanadi shekarun ritaya su kasance shekara 60 ko shekaru 35 na aiki.
Ƙorafin ya jaddada cewa umarnin zartarwa ba domin soke doka ba ne, balle gyaranta, sai dai aiwatar da ita.
Bugu da ƙari, mai ƙorafin ya yi watsi da dogaron gwamnan kan Dokar Buƙatar Dole, yana mai bayyana hakan a matsayin maras inganci a doka da harkokin gudanarwa.
Ya gargaɗi cewa wannan umarni na iya haifar da rikice-rikicen gudanarwa, zarge-zargen nuna wariya, da kuma ƙarar da ka iya gurgunta tafiyar da mulki.
Har ila yau, ƙorafin ya caccaki tsarin zaɓaɓɓen ƙarin wa’adin ga wasu mutane kawai, yana mai cewa Jihar Kano na da ƙwararrun ma’aikata da za su iya maye gurbin waɗanda wa’adinsu ya ƙare, ba tare da karya doka ba.
DanAbdullo ya buƙaci Majalisa da ta yi amfani da ikon sa ido da take da shi, domin soke wannan dokar zartarwa.
Ya yi gargaɗi cewa idan ba a yi hakan ba, hakan na iya zama tushen matsala da zai lalata tsarin aikin gwamnati a Kano.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Kano ma aikatan gwamnati an gwamnati
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Sake Gurfanar da Blatter Da Platini Kan Zargin Cin Hanci
Tsohon Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA), Sepp Blatter, da tsohon shugaban UEFA, Michel Platini, za su sake gurfana a gaban wata kotu a Switzerland kan zargin cin hanci da rashawa.
Kotun ɗaukaka ƙara da ke Muttenz za ta saurari buƙatar ofishin babban mai shigar da ƙara na ƙasar, wanda ke son sake dawo da tuhume-tuhumen da ake yi wa Blatter, mai shekaru 89, da Platini, mai shekaru 69.
Hasashe Kan Tarukan CPPCC Da NPC Na 2025 Kano Pillars Ta Koma Ta 4 A Teburin Firimiyar NijeriyaBlatter ya ce yana fatan kotun za ta tabbatar da sahihancin kwantiragin da ke tsakaninsa da Platini, kamar yadda wata kotu ta yi a shekarar 2022, lokacin da aka wanke su daga zargin cin hancin dala miliyan 2.1.
Blatter ya shugabanci FIFA daga 1998 zuwa 2015, kuma an yi tsammanin Platini ne zai gaje shi kafin shari’ar ta hana shi ci gaba da neman shugabancin hukumar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp