Aminiya:
2025-04-24@20:29:11 GMT

An miƙa wa Majalisar Kano ƙorafin ƙara wa’adin manyan ma’aikatan gwamnati

Published: 1st, February 2025 GMT

An miƙa wa Majalisar Dokokin Kano ƙorafi kan abin da aka bayyana a matsayin ƙarin wa’adin aiki na wasu manyan jami’an gwamnati ba bisa ƙa’ida ba.

A ƙunshin ƙorafin an yi zargin cewa ana ƙara wa manyan jami’an wa’adin aiki ta hanyar amfani da Dokar Zartarwa Ta 1 ta 2025, wadda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanyawa hannu.

A cikin wata wasika mai kwanan wata 6 ga Janairu, 2025, Sani Usman DanAbdullo, Esq., Daraktan Gudanarwa da Harkokin Gabaɗaya na Hukumar Yaki da Cutar Kanjamau ta Jihar Kano (KSACA), ya buƙaci Majalisa da ta kare doka da oda, tare da dakatar da abin da ya bayyana a matsayin rashin amfani da ikon zartarwa yadda ya kamata.

An aike da ƙorafin ne zuwa ga Kakakin Majalisar, Hon. Jibrin Ismail Falgore, da kuma Shugaban Kwamitin Majalisa kan Ƙorafe-ƙorafe na Jama’a.

Takardar ta ƙalubalanci Dokar Zartarwa da aka fitar a ranar 1 ga Janairu, 2025, wadda ake zargi da bayar da ƙarin shekaru biyu ga Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, Magatakardan Majalisa, wasu alƙalai, da ma’aikatan ɓangaren lafiya.

Ana iya tuna cewa Gwamna Yusuf ya amince da ƙarin wa’adin shekaru biyu ga Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, wasu Manyan Sakatarori, da manyan ma’aikatan gwamnati, wanda zai fara aiki daga 31 ga Disamba, 2024.

Gwamnan ya kare wannan mataki, yana mai cewa Dokar Buƙatar Dole (Doctrine of Necessity) ce ta tilasta hakan, yana mai dogaro da sassa 5(2) da 208 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999.

Sai dai a cikin ƙorafin, an bayyana cewa wannan umarni ya ci karo da dokokin jihar, musamman Dokar Fansho da Giratuti ta Jihar Kano (Gyara Na 5), 2024, wadda ta tanadi shekarun ritaya su kasance shekara 60 ko shekaru 35 na aiki.

Ƙorafin ya jaddada cewa umarnin zartarwa ba domin soke doka ba ne, balle gyaranta, sai dai aiwatar da ita.

Bugu da ƙari, mai ƙorafin ya yi watsi da dogaron gwamnan kan Dokar Buƙatar Dole, yana mai bayyana hakan a matsayin maras inganci a doka da harkokin gudanarwa.

Ya gargaɗi cewa wannan umarni na iya haifar da rikice-rikicen gudanarwa, zarge-zargen nuna wariya, da kuma ƙarar da ka iya gurgunta tafiyar da mulki.

Har ila yau, ƙorafin ya caccaki tsarin zaɓaɓɓen ƙarin wa’adin ga wasu mutane kawai, yana mai cewa Jihar Kano na da ƙwararrun ma’aikata da za su iya maye gurbin waɗanda wa’adinsu ya ƙare, ba tare da karya doka ba.

DanAbdullo ya buƙaci Majalisa da ta yi amfani da ikon sa ido da take da shi, domin soke wannan dokar zartarwa.

Ya yi gargaɗi cewa idan ba a yi hakan ba, hakan na iya zama tushen matsala da zai lalata tsarin aikin gwamnati a Kano.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Kano ma aikatan gwamnati an gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta yi ta’aziyya game da rasuwar Paparoma Francis

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya mika ta’aziyya game da  rasuwar shugaban ‘yan darikar katolika na duniya Paparoma Francis.

A wani sako da ya aike a jiya Litinin, Pezeshkian ya ce Paparoma Francis a matsayinsa na shugaban darikar Roman Katolika ya sadaukar da rayuwarsa gaba daya wajen yada koyarwar Yesu Almasihu.

Shugaban ya ce Paparoma ya yi kokari wajen samar da zaman lafiya a duniya, da yekuwar samar da adalci, da ‘yanci, da mu’amala da tsaro a tsakanin addinai.

Daya daga cikin shi ne bayyanannen matsayinsa na yin Allah wadai da kisan gillar da gwamnatin Isra’ila ke yi a Gaza da kuma kiran da ya yi na kawo karshen kisan kiyashin da ake yi wa mata da kananan yara Falasdinawan da ba su ji ba ba su gani ba.

A jiya Litini ce Cocin Vatican ta sanar da rasuwar shugaban majami’ar katolika na duniya, Fafaroma Francis yana da shekaru 88 a duniya.

A shekarar 2023 ne cocin ya zabi Fafaroman, wanda asalin sunansa shi ne Cardinal Jorge Mario Bergoglio a matsayin wanda zai jagorance ta, bayan saukar Fafaroma Benedict XVI daga kan mukamin.

Fafaroman ya rasu ne bayan fama da doguwar jinya, inda a baya ya shafe makonni a wani asibiti, inda aka bayyana cewa yana fama da sanyin hakarkari mai tsanani.

Francis, shi ne Paparoma na 266 na Cocin Roman Katolika, kuma an bayyana cewa ya rasu ne sakamakon bugun jini.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta amince ta bai wa mahajjata kuɗin guzirinsu a hannu
  • **Gwamnati Za Ta Kwace Gidajen Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya Ba Su Biya Bashin Gidaje Ba
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa
  • ‘Yan majalisar dokokin Aljeriya sun yi kira da a haramta daidaita alaka da Isra’ila
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna
  • An sanya dokar hana fita ta sa’o’i 12 a Neja
  • Iran ta yi ta’aziyya game da rasuwar Paparoma Francis
  • Sahel: CILSS ta yi gargadi game da sake bullar ‘’kwarin dango’’ a yankin sahel
  • Tinubu Ya Komo Nijeriya Bayan Ziyarar Mako 3 A Turai