Mun Samar Da Kyakkyawan Tsaro Ga Masu Yi Wa Kasa Hidima-NYSC
Published: 2nd, February 2025 GMT
Darakta-Janar na Hukumar yi wa kasa hidima ta kasa NYSC, Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa masu yi wa kasa hidima a fadin kasar nan cewa ba za a tura su yankunan da ke da kalubalen tsaro ba.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga matasa masu yi wa kasa hidima da ke samun horo a sansaninsu da ke Gusau, babban birnin jihar Zamfara.
Darakta Janar na NYSC wanda ke rangadi a sansanin masu yi wa kasa hidimar a jihar Zamfara, ya bayyana jin dadinsa kan yadda ak tsaurara matakan tsaro a sansanin.
Ya jaddada cewa, tsaro da jin dadin matasan na da matukar muhimmanci ga hukumar.
Birgediya Janar Ahmad ya jaddada bukatar matasan su kasance masu lura da tsaro a kodayaushe, tare da kaucewa tafiye-tafiye ba tare da wani kwakkwaran dalili ba.
Ya kuma ƙarfafa su da su koyi aaƙalla sana’o’i biyu kafin su bar sansanin domin su dogara da kansu bayan sun kammala yi wa kasa hidima.
A cewarsa, hukumar NYSC za ta ci gaba da yin duk mai yiwuwa don tabbatar da jin dadinsu, yana mai jaddada cewa, a kwanakin baya gwamnatin tarayya ta amince da karin alawus-alawus dinsu na wata wata.
“Gwamnatin tarayya, ta amince da karin alawus-alawus na ‘yan yi wa kasa hidima daga Naira 33,000 zuwa Naira 77,000 duk wata, muna kuma sa ran nan ba da dadewa ba za a fara aiwatar da hakan.
A nasa jawabin, Ko’odinetan NYSC a Jihar Zamfara, Malam Mohammed Lawan ya yaba wa Darakta-Janar na NYSC bisa jagorancinsa, da kuma yadda ya samar da kayan aikin da suka dace don ganin an gudanar da horaswar a jihar Zamfara cikin sauki da nasara.
Malam Lawan ya bayyana cewa, an yi wa matasa masu yi wa kasa hidima su 573 rajista a sansanin, suna kuma samun horo yadda ya dace.
Matasan sun gudanar da fareti da raye-rayen al’adu da sauransu yayin ziyarar Darakta-Janar din.
Daga Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Zamfara masu yi wa kasa hidima Darakta Janar
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Jana’izar Shugaban Kasar Namibia Da Ya Samo Mata ‘Yanci
A ranar Asabar din da ta gabata ne dai aka yi jana’izar Sam Nujoma wanda shi ne ya samo wa kasar ‘yanci bayan tsawon shekaru na gwgawarmaya.
Mahalarta jana’izar ta Nujoma sun kunshi iyalansa, mata,’ya’yan da jikokin, sai shugabannin kasashen Afirka na da, da masu ci.
A yayin jana’izar an bayyana Nujoma a matsayin wani gwarzo na fada da mulkin mallaka da tsarin wariya da ya kare nahiyar ta Afirka.”
Shugaban kasar Namibia mai ci a yanzu ya bayyana Nujoma da cewa; Gwarzo ne da za a rufe shi a cikin makabartar da gwarazan kasar suke kwance. Kuma shi na musamman ne daga cikin ‘ya’yan wannan kasa, sannan kuma dan juyin juya hali.
Mahalarta jana’izar dai sun fito ne daga kowace kusurwa ta kasar Namibia,inda su ka taru a makabartar da ake rufe gwarazan kasar a birnin Waindhoek, domin yin jinjina da ban girma na krshe ga tsohon shugaban kasar wanda ya rasu yana dan shekaru 95.
Nujoma ya yi shugabancin kasar a zango uku daga 1990 zuwa 2005, tare da shimfida zaman lafiya da tsaro a cikin kasar.
An dauki kwanaki 21 ana juyayin rasuwarsa a gwamnatance, tare da yin kasa-kasa da tutar kasar.