Mun Samar Da Kyakkyawan Tsaro Ga Masu Yi Wa Kasa Hidima-NYSC
Published: 2nd, February 2025 GMT
Darakta-Janar na Hukumar yi wa kasa hidima ta kasa NYSC, Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa masu yi wa kasa hidima a fadin kasar nan cewa ba za a tura su yankunan da ke da kalubalen tsaro ba.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga matasa masu yi wa kasa hidima da ke samun horo a sansaninsu da ke Gusau, babban birnin jihar Zamfara.
Darakta Janar na NYSC wanda ke rangadi a sansanin masu yi wa kasa hidimar a jihar Zamfara, ya bayyana jin dadinsa kan yadda ak tsaurara matakan tsaro a sansanin.
Ya jaddada cewa, tsaro da jin dadin matasan na da matukar muhimmanci ga hukumar.
Birgediya Janar Ahmad ya jaddada bukatar matasan su kasance masu lura da tsaro a kodayaushe, tare da kaucewa tafiye-tafiye ba tare da wani kwakkwaran dalili ba.
Ya kuma ƙarfafa su da su koyi aaƙalla sana’o’i biyu kafin su bar sansanin domin su dogara da kansu bayan sun kammala yi wa kasa hidima.
A cewarsa, hukumar NYSC za ta ci gaba da yin duk mai yiwuwa don tabbatar da jin dadinsu, yana mai jaddada cewa, a kwanakin baya gwamnatin tarayya ta amince da karin alawus-alawus dinsu na wata wata.
“Gwamnatin tarayya, ta amince da karin alawus-alawus na ‘yan yi wa kasa hidima daga Naira 33,000 zuwa Naira 77,000 duk wata, muna kuma sa ran nan ba da dadewa ba za a fara aiwatar da hakan.
A nasa jawabin, Ko’odinetan NYSC a Jihar Zamfara, Malam Mohammed Lawan ya yaba wa Darakta-Janar na NYSC bisa jagorancinsa, da kuma yadda ya samar da kayan aikin da suka dace don ganin an gudanar da horaswar a jihar Zamfara cikin sauki da nasara.
Malam Lawan ya bayyana cewa, an yi wa matasa masu yi wa kasa hidima su 573 rajista a sansanin, suna kuma samun horo yadda ya dace.
Matasan sun gudanar da fareti da raye-rayen al’adu da sauransu yayin ziyarar Darakta-Janar din.
Daga Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Zamfara masu yi wa kasa hidima Darakta Janar
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta jaddada cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Gudanar Da Tattaunawa Kan Tsaronta Ba
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa; Iran ba za ta taba gudanar da shawarwari kan tsaronta ba
A cikin jawabinsa na shirye-shiryen shirin zaman taron Carnegie kan manufofin nukiliya na kasa da kasa da aka soke a yanzu, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa kamfanonin Amurka za su iya cin gajiyar damar dala tiriliyan da tattalin arzikin Iran ke samarwa kuma kasuwar Iran za ta iya farfado da masana’antar nukiliyar Amurka da ta tsaya cak.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana ta shafinsa na Twitter a takaitaccen jawabin da aka shirya yi a taron manufofin nukiliya na kasa da kasa na Carnegie, yana mai jaddada cewa, “Iran sam ba ta da niyyar yin shawarwari da tattaunawa a fili a bainar jama’a.”
Araqchi ya ci gaba da cewa, “A cikin jawabinsa, ya kuma bayyana karara cewa wasu ‘kungiyoyin masu sha’awa na musamman’ na kokarin yin magudi tare da bata tsarin diflomasiyya ta hanyar bata sunan masu tattaunawan tare da yin kira ga gwamnatin Amurka da ta gabatar da bukatu mafi tsanani da girma.”