Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ya Raba Sama Da Miliyan 75 Ga Marasa Galihu
Published: 2nd, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce za a ci gaba da bada tallafi ga al’umma a dukkan mazabu 30 na ‘yan majalisar dokokin Jihar.
Gwamnan Jihar Malam Umar Namadi ya bada wannan tabbacin a lokacin da yake kaddamar da bada tallafi ga al’ummar karamar hukumar Miga wanda Shugaban majalisar dokokin Jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya raba fiye da Naira Miliyan 75 ga masu karamin karfi.
Malam Umar Namadi, ya yaba da tsarin bada tallafin ga al’ummar karamar hukumar ta Miga.
A cewarsa, tsarin bada wannan tallafi da kakakin majalisar ya yi ya dace da kudirorin gwamnatin jihar 12.
Yana mai nuni da cewar, a kowacce Karamar Hukuma za a kaddamar da irin wannan tallafi domin bunkasa tattalin arzikin al’umma don su zamo masu dogaro da kai.
Namadi, ya ce bullo da tsarin bada tallafin ya nuna cewar ‘yan majalisar Jihar suna tare da al’ummarsu.
Shi kuwa a nasa jawabin, Kakakin majalisar dokokin jihar Jigawan Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya ce rabon tallafin ya tasamma fiye da Naira Miliyan 75 wanda al’ummar mazabar Miga ne za su ci moriyar tsarin.
Ya ce tallafin zai basu damar kama sana’oi daban daban domin su zamo masu dogaro da kai.
Dangyatin, ya kuma bayyana cewar mutane kusan ne za su amfana da tallafin kudaden domin bunkasa tattalin arzikinsu.
Kakakin majalisar, ya kuma godewa Gwamna Umar Namadi bisa kyawawan kudurorinsa, gami da kulawarsa wajen ciyar da al’ummar jihar gaba.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
An miƙa wa Majalisar Kano ƙorafin ƙara wa’adin manyan ma’aikatan gwamnati
An miƙa wa Majalisar Dokokin Kano ƙorafi kan abin da aka bayyana a matsayin ƙarin wa’adin aiki na wasu manyan jami’an gwamnati ba bisa ƙa’ida ba.
A ƙunshin ƙorafin an yi zargin cewa ana ƙara wa manyan jami’an wa’adin aiki ta hanyar amfani da Dokar Zartarwa Ta 1 ta 2025, wadda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanyawa hannu.
A cikin wata wasika mai kwanan wata 6 ga Janairu, 2025, Sani Usman DanAbdullo, Esq., Daraktan Gudanarwa da Harkokin Gabaɗaya na Hukumar Yaki da Cutar Kanjamau ta Jihar Kano (KSACA), ya buƙaci Majalisa da ta kare doka da oda, tare da dakatar da abin da ya bayyana a matsayin rashin amfani da ikon zartarwa yadda ya kamata.
An aike da ƙorafin ne zuwa ga Kakakin Majalisar, Hon. Jibrin Ismail Falgore, da kuma Shugaban Kwamitin Majalisa kan Ƙorafe-ƙorafe na Jama’a.
Takardar ta ƙalubalanci Dokar Zartarwa da aka fitar a ranar 1 ga Janairu, 2025, wadda ake zargi da bayar da ƙarin shekaru biyu ga Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, Magatakardan Majalisa, wasu alƙalai, da ma’aikatan ɓangaren lafiya.
Ana iya tuna cewa Gwamna Yusuf ya amince da ƙarin wa’adin shekaru biyu ga Shugaban Ma’aikatan Gwamnati, wasu Manyan Sakatarori, da manyan ma’aikatan gwamnati, wanda zai fara aiki daga 31 ga Disamba, 2024.
Gwamnan ya kare wannan mataki, yana mai cewa Dokar Buƙatar Dole (Doctrine of Necessity) ce ta tilasta hakan, yana mai dogaro da sassa 5(2) da 208 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999.
Sai dai a cikin ƙorafin, an bayyana cewa wannan umarni ya ci karo da dokokin jihar, musamman Dokar Fansho da Giratuti ta Jihar Kano (Gyara Na 5), 2024, wadda ta tanadi shekarun ritaya su kasance shekara 60 ko shekaru 35 na aiki.
Ƙorafin ya jaddada cewa umarnin zartarwa ba domin soke doka ba ne, balle gyaranta, sai dai aiwatar da ita.
Bugu da ƙari, mai ƙorafin ya yi watsi da dogaron gwamnan kan Dokar Buƙatar Dole, yana mai bayyana hakan a matsayin maras inganci a doka da harkokin gudanarwa.
Ya gargaɗi cewa wannan umarni na iya haifar da rikice-rikicen gudanarwa, zarge-zargen nuna wariya, da kuma ƙarar da ka iya gurgunta tafiyar da mulki.
Har ila yau, ƙorafin ya caccaki tsarin zaɓaɓɓen ƙarin wa’adin ga wasu mutane kawai, yana mai cewa Jihar Kano na da ƙwararrun ma’aikata da za su iya maye gurbin waɗanda wa’adinsu ya ƙare, ba tare da karya doka ba.
DanAbdullo ya buƙaci Majalisa da ta yi amfani da ikon sa ido da take da shi, domin soke wannan dokar zartarwa.
Ya yi gargaɗi cewa idan ba a yi hakan ba, hakan na iya zama tushen matsala da zai lalata tsarin aikin gwamnati a Kano.