Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce za a ci gaba da bada tallafi ga al’umma a dukkan mazabu 30 na ‘yan majalisar dokokin Jihar.

Gwamnan Jihar Malam Umar Namadi ya bada wannan tabbacin a lokacin da yake kaddamar da bada tallafi ga al’ummar karamar hukumar Miga wanda Shugaban majalisar dokokin Jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya raba fiye da Naira Miliyan 75 ga masu karamin karfi.

Malam Umar Namadi, ya  yaba da tsarin bada tallafin ga al’ummar karamar hukumar ta Miga.

A cewarsa, tsarin bada wannan tallafi da kakakin majalisar ya yi ya  dace da kudirorin gwamnatin jihar 12.

Yana mai nuni da cewar, a kowacce Karamar Hukuma  za a kaddamar da irin wannan tallafi domin bunkasa tattalin arzikin al’umma don su zamo masu dogaro da kai.

Namadi, ya ce bullo da tsarin bada tallafin  ya nuna cewar ‘yan majalisar Jihar suna tare da al’ummarsu.

Shi kuwa a nasa jawabin, Kakakin majalisar dokokin jihar Jigawan Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya ce rabon tallafin ya tasamma fiye da Naira Miliyan 75 wanda al’ummar mazabar Miga ne za su ci moriyar tsarin.

Ya ce tallafin zai basu damar kama sana’oi daban daban domin su zamo masu dogaro da kai.

Dangyatin, ya kuma bayyana cewar mutane kusan ne za su amfana da tallafin kudaden domin bunkasa tattalin arzikinsu.

Kakakin majalisar, ya kuma godewa Gwamna Umar Namadi bisa kyawawan kudurorinsa,  gami da kulawarsa wajen ciyar da al’ummar jihar gaba.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummar Gaza Suna Tsananin bukatar Agaji Da Kiran A Tilastawa Gwamnatin Mamayar Isra’ila Bude Mashigar Yankin

Al’ummar Gaza sun bukaci kasashen duniya da su tilasta daukan matakin shigar da kayan agaji cikinsu

Al’ummar Falasdinawa a Zirin Gaza sun yi kira ga hukumomin kasa da kasa da na Larabawa da su tilasta shigar da kayan agaji cikin yankin, duba da munanan bala’in jin kai da al’ummar yankin ke fuskanta.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Akif al-Masri, kwamishinan hukumar koli ta al’amuran da suka shafi Falasdiwa a Gaza, ya ce: “Matsalar yunwa tana barazana ga rayuwar dubban daruruwan mutanen Gaza,  yana mai cewa: Mafi yawan gidaje kusan babu kayan abinci, kuma iyalai ba za su iya samun abincinsu na yau da kullum ba.”

Al-Masry ya tabbatar da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun ketare dukkan iyakokin kasa ta hanyar kai hare-hare wuce gona da iri kan wuraren dafa abinci da wuraren jin dadin jama’a, wadanda ke ba da taimako kadan ga matalauta da mabukata. Ya yi kira da a gaggauta bude mashigar kai daukin gaggawa zuwa Gaza, tare da ba da izinin gabatar da agajin jin kai, irin abinci, da magunguna cikin Gaza ba tare da wani bata lokaci ko sharadi ba, don ceton rayukan mutane da dama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shenzhou-20: Kasar Sin Ta Aike Da ‘Yan Sama Jannati 3 Zuwa Sararin Samaniya
  • An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe
  • Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa
  • An Bayyana Filin Jirgin Sama Minna a Matsayin Mafita Ga Jiragen da ke sauka Abuja
  • Gwamna Inuwa Ya Bayar Da Gudunmawar Naira Miliyan 10 Ga Iyalan Wadanda Hatsarin Ista Ya Rutsa Da Su A Gombe
  • Xi: Yake-yaken Haraji Da Kasuwanci Na Tauye Hakkoki Da Muradun Dukkan Kasashe
  • Al’ummar Gaza Suna Tsananin bukatar Agaji Da Kiran A Tilastawa Gwamnatin Mamayar Isra’ila Bude Mashigar Yankin
  • ‘Yan majalisar dokokin Aljeriya sun yi kira da a haramta daidaita alaka da Isra’ila
  • Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka
  • 2024: Manyan Alkaluman Sufuri 2 Na Filayen Jiragen Sama Na Kasar Sin Sun Kafa Tarihi