Shuwagabannin kungiyar kasashen raya tattalin arziki da kuma tsaron kasashen Afrika da kudu ta ce zasu ci gaba da wanzar da sojojinsu a kasar Congo duk tare da sauye-sauyen da kungiyar yan tawaye na M23 suka yi a yankin arewacin KIVU.

Shafin yanar gizo na Labarai ‘Africa News” ya bayyana cewa shuwagabannin kungiyar sun bada wannan sanarwan ne bayan wani taron gaggawa da suka gudanar a kasar Zibabwe a ranar Jumma’an da ta gabata.

Shugaban kungiyar na riko-riko kuma shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, ya yim kira ga kungiyar ta kasance mai nuna karfi da da kuma juriya kan abubuwanda da ke faruwa a arewacin congo.

Sojojin tabbatar da zaman lafiya na kungiyar a cikin makonnin da suka gabata sun fuskanci koma baya a hannun sojojin M23, inda suka kashe sojojin kungiyar kimani dozen guda daga kasashen na SADC.

Affirka ta kudu, Malawi, da Tanzania sun rasa sojoji a dai dai lokacinda sojojin M23 suka shiga birnin Goma babban birnin. A halin yanzu dai shugaba Tsetsekedi ya fara tattara sojojin kasar don kare birnin Kinshasa babban birnin kasar ta Congo.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Birnin Istambul Ta Dakatar Da Akram Imamoglu Daga Matsayinsa Na Magajin Garin Birnin

Hukumar birnin istambul ta bada sanarwan dakatar da Akram Imamoglu daga matsayinsa na magajin garin birnin Istambul na wucin gadi, har zuwa lokacinda za’a tabbatar da kubutarsa daga abubuwan da aka zarginsa da su.

Tashar talabijin ta Almayaddeen ta kasar Labanon ta nakalto mahukunta a birnin Istambul na bada labarin cewa za’a zabi wanda zai maye gurbinsa na wucin gadi a ranar Laraba mai zuwa.

Labarin ya kara da cewa ana zirgin Imamoglu da karban rashawa da cin hanci da kuma kafa kungiyar yan ta’adda.

Kama Imamoglu magajin garin na birnin Istambul dai a makon da ya gabata, ya sa dubban daruruwan masu goyon bayansa a birnin  Istambul da wasu birane a kasar suka fito kan tituna tare da bukatar a sake shi.

Ana ganin Imamoglu zai iya zaman dan takarar shugaban kasa wanda zai iya kada shugaba Ordugan a zaben shugaban kasa mai zuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul
  • Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falastinu a kasashen duniya
  • Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada
  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata
  • Hukumar Birnin Istambul Ta Dakatar Da Akram Imamoglu Daga Matsayinsa Na Magajin Garin Birnin
  • Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum