Leadership News Hausa:
2025-04-15@23:27:06 GMT

Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu

Published: 2nd, February 2025 GMT

Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu

Kungiyar kwallon kafa ta Real Balladolid ta zargi Manchester City da karfafa gwiwa ga daya daga cikin ‘yan wasanta, Juma Bah domin ya soke yarjejeniyarsa ya koma buga Premier League da buga wasa. Dan wasan mai tsaron baya, ya sanar da kungiyar ta Sifaniya ranar Talata cewar yana so ya katse yarjejeniyarsa, saboda ya koma Manchester City kan kankanin kudi.

Tun a baya Manchester City ta nemi izinin Balladolid, domin tattaunawa kan sayen matashin mai shekara 18, domin ya koma buga mata wasa amma sai kungiyar ta ce tana son dan wasanta kuma ba na sayarwa bane. Bah bai halarci atisaye ba ranar Laraba ba, inda hukumar kwallon kafar Sifaniya ta tabbatar cewar ya biya sauran kunshin kwantiraginsa a kungiyar, domin ya kara gaba.

Hadin Lemon Tsamiya (Tamarin Juice) AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin Rukuni

Balladolid ta ce matakin da matashin ya dauka Manchester City ce da wakilin dan wasan suka kitsa komai, ta kuma yi Alla-wadai da wannan lamarin. Dan wasan mai shekara 18 ya koma kungiyar kwallon kafa ta Balladolid daga AIK Freetong, domin buga wasannin aro a bara, inda a watan nan Balladolid ta mallaki dan wasan bayan ya yi kokari kuma ya burge masu koyar da kungiyar. Sai dai Bah yana kan tsarin yarjejeniya ta matashin dan wasa, amma bai amince ya saka hannu ba kan kwantiragi a matakin kwararren dan wasa ba.

Balladolid ta ce za ta dauki mataki na shari’a kan Bah, za kuma ta yi dukkan abin da ya kamata domin ta kare martabarta amma kuma har yanzu kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ba ga ce komai ba a kan zargin da ake mata na hurewa Bah kunne

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar

Babban sakataren kungiyar kasashen Larabawa na yankin tekun Farisa (PGCC) ya yi fatan alkhairi ga kasashen Iran da Amurka a tattaunawa ba kai tsaye ba a tsakaninsu dangane da shirin Nukliya ta kasar Iran na zaman lafiya wanda suka fara, a birnin Mascat na kasar Omman a ranar Asabar da ta gabata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Jasem Mohamed AlBudaiw yana fadar haka a jiya Lahadi ya kuma kara da cewa, kungiyar tana bukatar gidan an warware matsaloli tsakanin kasashen duniya ta hanyar tattanawa.  Haka ma tsakanin kasashen yankin.

AlBudaiw ya yabawa kasar Omman da shirya wannan tattaunawar, sannan ya yi fatan tattaunawan da aka fara zai kai ga rage tada jijiyoyin wuya a yankin da kuma kasashen duniya, ya kuma ce kasashen yankin suna fatan zasu kai ga sakamako mai kyau tsakanin kasashen biyu.

Gwamnatin kasar Iran dai tana har yanzun suna shakkar kasar Amurka saboda yawan yaudarar da tayiwa kasar a baya. Musamman fitar kasar daga yarjeniyar JCPOA a shekara ta 2018. Da kuma yawan takunkuman da ta dorawa a kasar tun lokacin.

Daga karshe babban sakataren kungiyar ta PGCC ya ce tana fatan za’a kawo karshen duk wani rikici a gabas ta tsakiya daga ciki har da na HKI a falasdinawa a Gaza ta hanyar tattaunawa da fahintar Juna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Isa Kuala Lumpur Domin Ziyarar Aiki A Malaysia
  • Kotu Ta Tsare Matasa 2 Kan Wallafa Bidiyon Batsa A TikTok A Kano
  • EFCC Ta Gurfanar Da Ɗan China A Kotu Kan Bayar Da Bayanan Ƙarya
  • Ministan Harkokin Noma Na Kasar Iran Ya Kama Hanya Zuwa Kasar Brazil
  • Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi
  • Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara