Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu
Published: 2nd, February 2025 GMT
Kungiyar kwallon kafa ta Real Balladolid ta zargi Manchester City da karfafa gwiwa ga daya daga cikin ‘yan wasanta, Juma Bah domin ya soke yarjejeniyarsa ya koma buga Premier League da buga wasa. Dan wasan mai tsaron baya, ya sanar da kungiyar ta Sifaniya ranar Talata cewar yana so ya katse yarjejeniyarsa, saboda ya koma Manchester City kan kankanin kudi.
Tun a baya Manchester City ta nemi izinin Balladolid, domin tattaunawa kan sayen matashin mai shekara 18, domin ya koma buga mata wasa amma sai kungiyar ta ce tana son dan wasanta kuma ba na sayarwa bane. Bah bai halarci atisaye ba ranar Laraba ba, inda hukumar kwallon kafar Sifaniya ta tabbatar cewar ya biya sauran kunshin kwantiraginsa a kungiyar, domin ya kara gaba.
Hadin Lemon Tsamiya (Tamarin Juice) AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin RukuniBalladolid ta ce matakin da matashin ya dauka Manchester City ce da wakilin dan wasan suka kitsa komai, ta kuma yi Alla-wadai da wannan lamarin. Dan wasan mai shekara 18 ya koma kungiyar kwallon kafa ta Balladolid daga AIK Freetong, domin buga wasannin aro a bara, inda a watan nan Balladolid ta mallaki dan wasan bayan ya yi kokari kuma ya burge masu koyar da kungiyar. Sai dai Bah yana kan tsarin yarjejeniya ta matashin dan wasa, amma bai amince ya saka hannu ba kan kwantiragi a matakin kwararren dan wasa ba.
Balladolid ta ce za ta dauki mataki na shari’a kan Bah, za kuma ta yi dukkan abin da ya kamata domin ta kare martabarta amma kuma har yanzu kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ba ga ce komai ba a kan zargin da ake mata na hurewa Bah kunne
এছাড়াও পড়ুন:
Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
Shugaban kasar na Amurka Donald Trump ya wallafa wani sako a shafinsa na “Truth Social” da a ciki ya bayyana Volodymyr Zelenskyy dad an kama-karya, kuma abinda ya fi yi masa alheri shi ne ya yi wani abu da sauri, domin idan ba haka ba,zai yi asarar kasarsa baki daya.
Shugaban na kasar Amurka ya kara da cewa; Volodymyr Zelenskyy ya sa Amurka ta kashe dala biliyan 350 da ya shiga cikin yakin da ba zai iya samun nasara ba.
Har ila yau, shugaban na Amurka ya ce, shi kanshi Volodymyr Zelenskyy ya yi furuci da cewa, rabin kudaden da mu ka aika masa sun bace, kuma ya ki gudanar da yin zabe, don haka masu goyon bayansa ‘yan kadan ne.”
Bugu da kari Trump ya ce, ko kadan bai kamata a ce yaki ya barke ba, domin yaki ne da babu yadda za a yi ya yi nasara ba tare da goyon bayan Amurka da kuma Trump ba, yana mai yin ishara da cewa, ahalin yanzu Amurka tana tattaunawa cikin nasara da Rasha domin kawo karshen yakin.”
Wani sashe na sakon Trump din ya kunshi cewa; Ina son kasar Ukiraniya, sai dai abinda Volodymyr Zelenskyy ya yi, ya munana, ya ruguza kasarsa, kuma miliyoyin mutane sun mutu ba tare da dalili ba.
A gefe daya, kasashen turai sun mayar da martani akan maganganun na Trump, inda shugaban gwamantin Jamus ya ce shugaban kasar ta Ukiraniya ba dan dan kama-karya ba ne.