Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu
Published: 2nd, February 2025 GMT
Kungiyar kwallon kafa ta Real Balladolid ta zargi Manchester City da karfafa gwiwa ga daya daga cikin ‘yan wasanta, Juma Bah domin ya soke yarjejeniyarsa ya koma buga Premier League da buga wasa. Dan wasan mai tsaron baya, ya sanar da kungiyar ta Sifaniya ranar Talata cewar yana so ya katse yarjejeniyarsa, saboda ya koma Manchester City kan kankanin kudi.
Tun a baya Manchester City ta nemi izinin Balladolid, domin tattaunawa kan sayen matashin mai shekara 18, domin ya koma buga mata wasa amma sai kungiyar ta ce tana son dan wasanta kuma ba na sayarwa bane. Bah bai halarci atisaye ba ranar Laraba ba, inda hukumar kwallon kafar Sifaniya ta tabbatar cewar ya biya sauran kunshin kwantiraginsa a kungiyar, domin ya kara gaba.
Hadin Lemon Tsamiya (Tamarin Juice) AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin RukuniBalladolid ta ce matakin da matashin ya dauka Manchester City ce da wakilin dan wasan suka kitsa komai, ta kuma yi Alla-wadai da wannan lamarin. Dan wasan mai shekara 18 ya koma kungiyar kwallon kafa ta Balladolid daga AIK Freetong, domin buga wasannin aro a bara, inda a watan nan Balladolid ta mallaki dan wasan bayan ya yi kokari kuma ya burge masu koyar da kungiyar. Sai dai Bah yana kan tsarin yarjejeniya ta matashin dan wasa, amma bai amince ya saka hannu ba kan kwantiragi a matakin kwararren dan wasa ba.
Balladolid ta ce za ta dauki mataki na shari’a kan Bah, za kuma ta yi dukkan abin da ya kamata domin ta kare martabarta amma kuma har yanzu kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ba ga ce komai ba a kan zargin da ake mata na hurewa Bah kunne
এছাড়াও পড়ুন:
Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta
4 – Kar ki kasance kullum a cikin bacin rai ko fushi da mijinki, domin fushi kofa ce ta kowane sharri.
5 – Kar ki kasance mai girman kai wajen bashi hakkokin zamanku, abin da yake so ko da baki so matukar bai saba wa addini ba ki yi masa.
6 Ki nuna wa mijinki komai naki nasa ne komai nasa kuma nasa ne, ki nuna baki da iko a kai sai abin da ya yi.
7- Ki kasance mai kula da abubuwan da yake dubawa a jikinki in ya shigo gida, ina idonsa ke kallo a jikinki. Bayan kin yi kwalliya. sai a gyara masa su da kyau domin a dauke masa hankali. In kuma kin tabbatar duk lokacin da ya dawo yana neman buta ne, to ki kula da sanya ruwa a cikin butar.
8 – Ki kasan ce mai yawan godiya kan duk abin da ya kawo miki gida komai kankantar abin kar ki raina, sannan ki nuna masa kokarinsa a kan bin da ya kawo.
9 – Kar ki sake ko ki yi kasa a gwiwa wajen girmama duk wadanda kika san yana girmama su, kama daga iyaye har ‘yan uwa da abokan arzikinsa.
10- Kar ki yawaita tambayarsa daga ina kake ko me kake yi sai yanzu kake dawowa?
Ki kasance mai boye sirrinsa wajen iyayenki da sauran al’umma. 11 – Kar ki yarda duk lokacin da ya kiranki ki kawo masa wani abu ki tura wani ko wata ta kawo, ki je ki yi da kanki. Wadan abubuwa idan kika daure kina yi lallai za ki samu namiji a hannunki kamar dan jariri. Allay a ba da ikon yi
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp