Ministocin harkokin waje da wasu jami’an gwamnatocin kasashen sun ki amincewa da korar Falasdinawa daga kasarsu kamar yadda shugaban AMurka Donal Trump ya bada shawara.

Tashar talabijib ta Presstv a nan Tehran ya nakalto ministoci da jami’an gwamnatin kasashen kungiyar kasashen larabawa suna fadar haka, a wani taron hadin giuwa a cibiyar kungiyar dake birnin Alkahira na kasar Masar.

Labarin ya kara da cewa taron ya sami halattar ministocin harkokin waje na kasashe Masar, Jordan, Saudia, Qatar, da gwamnatin Palestinian Authority, sannan da wakilia daga sauran kasashen kungiyar ta ‘Arab League’ .

Kungiyar ta bayyana cewa kasashen kungiyar basy amince da duk wani kokari na canza yadda kasashen larabawa suke ciki don tabbatar da samuwar HKI a yankin ba, kamar yadda gwamnatin shugaba Trump take son ta yi ba.

Dangane da wannan gwamnatin kasar Saudiya ta da gwamnatin kasar Faransa zasu za su dauki nauyin gudanar da taro na musamman kan wannan shawara da shugaban kasar Amurka ya gabatar a cikin watan yuni mai zuwa. Sannan zasu karfafa shawarar samar da kasashe biyu a kan kasar Falasdinu da aka mamaye, a matsayin hanya tilo ta warwaren wannan matsalar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet

Jagoran ‘yan adawar Isra’ila Yair Lapid ya yi kira da a gudanar da zanga-zangar gama-gari idan Firaministan kasar Benjamin Netanyahu ya ki bin hukuncin da kotun kolin kasar ta yanke na dakatar da matakin da gwamnatinsa  na korar shugaban hukumar tsaron cikin gida ta Shin Bet.

 Yair Lapid ya shaidawa dubban masu zanga-zanga a Tel Aviv cewa “Idan har gwamnatin 7 ga watan Oktoba ta yanke shawarar kin yin biyayya ga hukuncin kotun, to za ta zama haramtacciyar gwamnati a wannan rana.”

“Dole ne tattalin arzikin kasar ya tsaya cik, majalisa ta shiga yajin aiki, kotu ta shiga yajin aiki, hukumomi su shiga yajin aikin, ba jami’o’i kadai ba, har da makarantu.” Inji shi.

A ranar Juma’a ne Kotun kolin Isra’ila ta dakatar da matakin da gwamnati ta dauka na korar shugaban Shin Bet, Ronen Bar, wanda ba a taba ganin irinsa ba, wanda sanarwar korar tasa ta sake haifar da baraka a tsakanin al’umma.

Amma Netanyahu ya dage kan cewa,”Ronen Bar ba zai ci gaba da zama shugaban Shin Bet ba, ba za a yi yakin basasa ba, kuma Isra’ila za ta ci gaba da kasancewa a matsayin kasa ta dimokuradiyya,” in ji shi a cikin wani sakon bidiyo inda yake kalubalantar Kotun Koli.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa
  • Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
  • Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet
  • Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban
  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  
  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Game Da Tunanin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam Da Kin Amincewa Da Siyasantar Da Hakkin Dan Adam
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • Cibiya Mai Fafutukar Kare Hakkokin Falasdinawa “Global 195” Ta Shelanta Farautar Sojojin HKI Da Su KaTafka Laifukan Yaki