Mahaifin ma’aikacin Aminiya ya rasu
Published: 2nd, February 2025 GMT
Allah Ya yi wa mahaifin ma’aikacin Aminiya, Abubakar Abdurrahman Adoro, rasuwa.
Mahaifin nasa, Farfesa Abdurrahman Lawal Adoro, ya rasu ne a gidansa da ke garin Batagarawa a Jihar Katsina, ranar Litinin 27 ga watan Janairu, 2025, a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Katsina, ya yi fama da jinya na wani lokaci.
Marigayi Shehin Malami a Sashen Harshen Larabci na Jami’ar Umaru Musa Yar’adua da ke Jihar Katsina, inda a nan ya samu matsayin Farfesa.
Ya kasance Shugaban Sashen Larabci (HOD) na Jami’ar na farko tun da aka kirkiro ta a shekarar 2006, inda ya yi wa’adi biyu na tsawon shekara goma zuwa 2016.
Shi ne mutum na farko ɗan asalin Jihar Katsina da ya samu muƙamin Farfesa a fannin harshen Larabci.
Haka kuma yana daga cikin malaman da suka ƙaddamar da Kungiyar Jama’atu Izalatul Bid’a Ka Ikamatis Sunnah (JIBWIS) a Jihar Katsina.
An haife shi a ranar 15 ga Fabrairu, 1953 unguwar Adoro da ke garin Katsina, kuma ya rasu yana da shekara 72, ya bar ’ya’ya 10 da jikoki 32.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Katsina
এছাড়াও পড়ুন:
Sharhi: Tattaunawa Zagaye Na Farko Tsakanin Iran Da Amurka A Oman
Sharhin zai yi dubi ne game da tattaunawar da aka fara gudanarwa zagaye na na farko tsakanin Iran da Amurka a birnin Mascut fadar mulkin kasar Oman, inda gwamnatin kasar Oman din take shiga tsakani a wannan tattaunawa wadda aka fara gudanarwa.
Tun da safiyar Asabar ne dai ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci ya isa birnin Mascut na kasar Oman da can ne za a yi tattaunawar da ba ta gaba da gaba ba a tsakanin jamhuriyar musulunci da Amurka.
Jim kadan bayan isar tasa birnin Mascut ministan harkokin wajen na jamhuriyar musulunci ta Iran ya gana da mai masaukinsa Sayyid Badar al-Busa’idi,inda ya mika masa takardu akan mahangar Iran.
A yayin ganawar da bangarorin biyu su ka yi, ministan harkokin wajen Iran ya yaba da matsayar Oman akan batutuwa da dama su ka shafi wannan yankin na yammacin Asiya.
Daga cikin masu yi wa ministan harkokin wajen na Iran rakiya da akwai mataimakinsa a fagen dokokin kasa da kasa Kazim Garib Abadi, kamar yadda kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Dr. Isma’ila Baka’i ya ambata.
Iran da Amurka suna tattaunawa ne ta hanyar shiga tsakanin kasar Oman ba ta gaba da gaba.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baqaei ya bayyana cewa, kwana guda gabanin tattaunawar a kasar Oman tsakanin Amurka da Iran kan shirin nukiliyar kasar Iran, akwai damammaki da dama na diflomasiyya da Amurka za ta iya tabbatar da aniyarta a kansu
Baqaei ya rubuta a dandalin X cewa, “Ya kamata Amurka ta mutunta wannan shawarar da aka yanke duk da cewa ana fama da rikici.”
“Ba za mu yanke hukunci ba, Muna da niyyar tantance niyyar dayan bangaren kuma za mu tabbatar da hakan a wannan tattaunawa,” in ji jami’in diflomasiyyar na Iran, ya kara da cewa Iran “za ta yi tunani kuma ta mayar da martani ga kowane mtaki.”
A ranar Litinin din makon da ya gabata ne shugaban Amurka Donald Trump ya ba da sanarwar cewa gwamnatinsa za ta shiga tattaunawa da Iran.
Kafin zuwa ga wannan tattaunawar dai bangarorin biyu sun yi musayar kalamai masu zafi, inda Trump ya yi barazanar daukar matakin soji idan tattaunawar ta ci tura.
Dangane da gargadin na Trump, wani babban mataimaki ga jagoran Iran Ayatollah Sayyed Ali Khamenei ya ce Iran za ta iya daukar dukkanin matakan da ta ga sun dace a kan wannan lamari.
Ganawar ta ranar Asabar na zuwa ne biyo bayan wata wasika da Trump ya aikewa Sayyed Khamenei a watan da ya gabata, inda ya bukaci Tehran da ta shiga tattaunawa, tare da yin gargadin cewa matakin soji na kan teburi idan Iran ta ki amincewa.
Tehran ta bayyana aniyar ta na shiga tattaunawar kai tsaye amma muddin Washington ta ci gaba da aiwatar da manufofinta na matsin lamba mafi tsanani a kan Iran, to kuwa tabbas wannan tattaunawa ba za ta iya haifar da da mai ido ba.
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya ce Amurka na da masaniya kan irin karfin kare kai da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ke da shi, yayin da ya ce kasar ta shirya tsaf domin kare kanta.
Ya kuma jaddada cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta yarda da Washington ba, amma duk da haka za ta gwada ta yayin tattaunawar,” in ji Abbas Araghchi.
Babban jami’in diflomasiyyar ya bayyana cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta neman yaki, amma idan ya zama dole ta san yadda za ta kare kanta. »
“Muna da shaku kan aniyar Amurka kuma ba mu da tabbacin cewa suna da niyyar gudanar da tattaunawa ta gaske, amma za mu gwada su.”
Haka nan kuma jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi watsi da zargin kasashen yamma – karkashin jagorancin Washington – cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran na neman mallakar makamin nukiliya.
Ya ce zargin da ake yi wa Iran na neman mallakar makamin nukiliya, zargi ne mara tushe balantana makama.
Dangane da bayanan da aka yi ta yadawa musamman daga bangaren mahukuntan Amurka na cewa tattaunawar za ta gudana ne tsakanin Iran da Amurka gaba da gaba, Araghchi ya bayyana imaninsa cewa irin matakan da Iran ta dauka a baya-bayan nan dangane da wannan tattaunawa wani babban yunkuri ne na diplomasiyya.
Ya fayyace cewa sabanin wasu fassarori da aka yi a baya-bayan nan a game da batun tattaunawa tsakanin kasashen biyu, inda ya ce kokarin bayyana ra’ayi ne na gaskiya da bude hanyar diflomasiyya.
Dangane da kalaman Trump da ya yi a ranar litinin, Araghchi ya bayyana cewa Iran a shirye take domin ganin an cimma matsaya, inda za ta halarci tattaunawa a kasar Oman a ranar Asabar.
Ya kuma kara da cewa, wannan ba sabon lamari ba ne, domin ita kanta Amurka tana tsakiyar yin shawarwari kai tsaye game da batun Rasha da Ukraine, batun da ya fi zafi da sarkakiya ta fuskar siyasa da tattalin arziki a mataki na kasa da kasa.