Aminiya:
2025-03-26@12:18:31 GMT

Asibitin Malam Aminu Kano ya hana motoci masu baƙin gilas shiga harabarsa

Published: 2nd, February 2025 GMT

A wani mataki na tsaro da Asibitin Koyarwa na Malam Aminu da ke Kano ya fitar saboda magance barazanar tsaro da yake fuskanta, ya fara aiwatar da dokar hana motoci masu baƙin gilas wato tinted glass shiga harabar asibitin.

Mahukuntan asibitin sun bayyana cewa, motocin da ke ɗauke da marasa lafiya ko ma’aikata za su iya shiga, amma sai an bi ka’idojin tsaro na musamman.

Mahaifin ma’aikacin Aminiya ya rasu Majalisar Matasa ta Ƙasa ta goyi bayan taron Kur’ani

A wata sanarwa da Daraktan Gudanarwa na asibitin, Usman Rabiu Mudi ya fitar, ya ce, an kafa dokar hana motocin masu baƙin gilashi shiga ne saboda wasu munanan abubuwan da suka faru.

Ya bayyana irin munanan ababen kamar yunƙurin sace mutane ta amfani da irin waɗannan motocin da kuma aikata ayyukan laifi daban-daban da suka ƙunshi sata da aikata abubuwan da ba su dace ba a cikin harabar asibitin.

Sanarwar ta ƙara da cewa, ma’aikatan asibitin da ke amfani da mota za su yi rajistar motocinsu a ofishin tsaro don samun tambarin tantancewa da izinin shiga.

A cewar rahotanni, satar motoci da babura da sauran kayayyaki masu daraja ta yi yawa a cikin harabar asibitin.

Haka kuma, an gano cewa, wasu mutane na amfani da harabar asibitin wajen aikata ayyukan ashsha, wanda hakan ya sa mahukuntan suka ɗauki wannan mataki na hana motoci masu baƙin gilashin shiga, don kare rayukan ma’aikata da marasa lafiya da baki.

Wani ɗalibi mai suna Ahmad Bala, wanda ya zo asibitin da mota mai baƙin gilashi, an dakatar da shi daga wurin jami’an tsaron da ke bakin ƙofa.

Ya ce, wannan doka tana da amfani, amma ya buƙaci a cire dalibai daga dokar.

“An dakatar da ni saboda baƙin gilashi, amma ni ɗalibi ne kuma ina goyon bayan wannan mataki.

“Amma ina ganin ya kamata a cire ɗalibai daga wannan doka saboda wannan asibitin koyarwa ne, kuma ɗalibai da dama suna zaune a cikin harabar asibitin,” in ji Bala.

Shugaban tsaro na asibitin, Sani Ahmad Mahmud ya bayyana cewa, matakin hana shigar motoci masu baƙin gilashin yana cikin manufofin kare ma’aikata da marasa lafiya da baƙi da ke zuwa asibitin.

“Wannan mataki ya zama wajibi saboda ƙalubalen tsaro da muke fuskanta. Ina kira ga jama’a su bi wannan doka tare da girmama ta, domin matakin yana cikin muradinsu,” in ji Mahmud.

Wasu daga cikin jama’a sun yaba da matakin, suna ganin hakan zai rage yawaitar shigar miyagun mutane cikin asibitin, inda suke amfani da damar babban harabar wajen aikata laifuka da ayyukan da ba su dace ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: harabar asibitin

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamishinan Tsaron Cikin Gida Na Kano Ya Yi Murabus Watanni 7 Bayan Naɗa Shi

 Kwamishinan tsaron cikin gida da ayyuka na musamman na jihar Kano, Manjo Janar Muhammad Inuwa Idris (mai ritaya), ya yi murabus daga mukaminsa. An tabbatar da murabus din nasa ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar. Ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da murabus din a hukumance, inda ya nuna jin dadinsa da irin gudunmawar da Janar din sojan ya bayar a lokacin da yake gudanar da aikinsa. Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea Kasuwar Kayayyakin Masarufi Ta Sin Za Ta Ci Gaba Da Nuna Yanayin Bunkasa Bisa Daidaito A Bana LEADERSHIP ta ruwaito cewa, Manjo janar Idris (mai ritaya) shi ne mamba na biyu a majalisar zartarwa ta jihar Kano da ya mika takardar murabus dinsa a shekarar 2025. In ba a manta ba, kwamishinan sa ido da tantance ayyuka, Mohammed Diggol, shi ma ya yi murabus a farkon wannan shekarar. An nada Manjo Janar Idris ne a watan Agustan 2024 a matsayin kwamishinan sabuwar ma’aikatar da aka kirkiro. A cikin dan kankanin wa’adinsa, ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa tsarin gudanar da ayyukan ma’aikatar. A cikin sanarwar a hukumance, gwamna Yusuf ya yabawa Manjo janar Idris bisa jajircewarsa da yi wa jihar hidima. “Muna godiya ga Manjo Janar Muhammad Inuwa Idris (mai ritaya) bisa jajircewa da bayar da gudunmawa wajen ci gaban jihar Kano tun daga lokacin da ya ke aikin soja, muna masa kyakkyawan fata a cikin sabuwar rayuwarsa ta gaba,” in ji gwamnan. Duk da cewa ba a bayar da wani dalili na murabus din nasa na ba zato ba tsammani ba, gwamnan ya bayyana kwarin gwiwar cewa, magajinsa zai dora kan harsashin da Idris ya kafa domin ganin ma’aikatar ta yi aiki yadda ya kamata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamishinan Tsaron Cikin Gida Na Kano Ya Yi Murabus Watanni 7 Bayan Naɗa Shi
  • Rikicin Masarauta: Duk mai ja da hukuncin Allah ba zai yi nasara ba — Sanusi II
  • Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • An Ɗauko Sojoji Daga Waje Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  • An Ɗauko Sojoji Daga Wajen Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  • UNRWA : hana shigar da kayan agaji Gaza, ya jefa yankin cikin matsanancin hali
  • NDLEA Ta Kama Ƴar Indiya Ɗauke Da Hodar Iblis A Kano
  • Wata mata ta haifi jaririn da ba nata ba
  • An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano