Masar Ta Yi Kira Ga HKI Da Ta Janye Sojojinta Daga Kudancin Lebanon
Published: 2nd, February 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Masar ta fitar da sanarwa da a ciki ta bukaci Isra’ila da ta janye sojojinta daga kudancin Lebanon tana mai cewa wannan wani abu ne mai matukar muhimmanci.
Ministan harkokin wajen kasar ta Masar Badar Abdulatif ya ce, wajibi ne ga Isra’’ila da ta janye sojojin nata daga Lebanon ba tare da wani sharadi ba, domin ba za a kyale ta akan koda taku daya na kasar Lebanon ba.
A karkashin sharadin tsagaita wutar yaki da aka yi a ranar 27 ga watan Nuwamba na 2024, Isra’ila za ta janye sojojinta daga cikin kasar ta Lebanon a ranar 26 ga watan nan na Janairu.
Ya zuwa yanzu dai an tura sojojin Lebanon da kuma na MDD a cikin garuruwan dake kan iyaka da Falasdinu dake karkashin mamaya,sai dai duk da hakan HKI tana ci gaba da zama a cikin wasu gargruwan na wannan yankin.
A makon da ya shude ne dai Amurka da kuma gwamnatin Lebanon su ka karawa Isra’ila wa’adin zuwa 18 ga watan Fabrairu domin su janye daga kasar.
Ministan harkokin wajen kasar ta Masar ya ce, ci gaba da zaman sojojin HKI a cikin Lebanon ya sabawa doka, kuma babu wani dalili da zai sa ta rika kai wa farafen hula hare-hare.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Ta Siyo Man Jiragen Sama Fiye Da Ganga Miliyan 2 Daga Matatar Dangote
Amurka ta shigo da sama da ganga miliyan biyu na man jiragen sama daga matatar Dangote a watan Maris. Matatar ta tabbatar da hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, inda ta ce hakan ya tabbatar da “nagartar da ba ta misaltuwa” na kayayyakin matatar da kuma aminci da kasashen duniya suka bai wa matatar. Nijeriyar Jiya Da Yau: Kiki-Kakar Sabgar ‘Yan Majalisu Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya Duba daga rahoton ma’aikatar sa ido kan zirga-zirgar jiragen ruwa ta Kpler, ta ce jiragen ruwa shida dauke da kusan ganga miliyan 1.7 na man jiragen sama daga matatar Dangote sun isa tashoshin jiragen ruwa na Amurka a wannan watan na Maris. Wani jirgin ruwa, Hafnia Andromeda, ana kyautata tsammanin zai isa tashar Everglades a ranar 29 ga Maris tare da kusan ganga 348,000 na man jirgin sama daga matatar Dangote.Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp