HausaTv:
2025-03-26@03:15:14 GMT

 Ana Ci Gaba Da Yi Wa Mutane Kisan Gilla A Kasar Syria

Published: 2nd, February 2025 GMT

Rahotanni da suke fitowa daga kasar Syria sun ce, ana ci gaba da yi wa daidaikun mutane kisan gilla a sassan kasar mabanbanta.

A kusa da garin Hamah, an kashe mutane 7 a bayana nan,  bayan da wasu masu dauke da makamai su ka shiga cikin garin Tal-Zahab. Masu dauke da bindigar sun kutsa gidan fararen hula tare da bude wuta a kansu.

Haka nan kuma maharan sun yi sata a cikin gidajen da su ka shiga.

An gano gawawwakin mutane 7 a cikin wadannan gidajen bayan ficewar maharan.  An harbi mutanan ne dai a kai da hakan ya yi sanadiyyar rasuwarsu.

Kamfanin dillancin larabdun “Sputnik” ya nakalto cewa, masu dauke da makaman sun kuma kame mutane da dama daga cikin wanann garin, tare da tafiyar da su zuwa wani  wuri da ba a san ko ina ne.

Da akwai tsoron cewa za a kashe wadannan mutanen da aka kama.

Wanann dai ba shi ne karon farko ba da ake yi wa fararen hula kisan gilla saboda banbancin akidarsu.

A bayan nan an kashe Dr. Hassan Ibrahim wanda yana daya daga cikin muhimman masu nazari da bincike a fagen ilimin kimiyya na kasar Syria, an kuwa tsinci gawarsa ne a garin “Ma’ariba” dake bayan birnin Damascus a ranar Asabar din da ta gabata. An kuma ga alamun azabtarwa kafin a kashe shi a sassan jikin nashi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata

Ma’aikatar kasuwanci ta kasar Afganistan ta bada sanarwan cewa kasar Iran ce a gaba da dukkan kasashen makobta da kasar Afganisatan wacce tafi shigo da kayakinta cikin kasar a shekara ta 1403 ta kalandar Iraniyawa da ta kare.

Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya nakalto kakakin ma’aikatar kasuwanci ta kasar Afganistan Abdussalam Jawad Okhande-Zadeh ya na fadar haka a yau Lahadi:

Ya kuma kara da cewa, kasashen da suka shigo da kayaki a kasar Afganistan a shekarar da ta gabata sun hada ta Iran, a gaba da ko wace kasa, sannan Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), Pakisatn, China da kuma Turkamanistan.

Kakakin ma’aikatar kasuwancin ta kasar Afganisatn ya ce a dayan bangaren kuma kasar Afaganista ta fidda kayaki zuwa kasashen waje wadanda kimarsu ya kai dalar Amurka biliyon guda a shekarar da ta gabata, kuma sun hada da busassun yayan itace, da darduma, da awduga da duwatsu masu daraja.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC
  • Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo
  • Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul
  • Hamas : Isra’ila ta yi amfani da sulhu wajen tattara bayanai kan shugabannin Hamas domin kashe su
  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24
  •  Shugaban Majalisar Dokokin Lebanon Ya Yi Gargadi Akan Masu Tunanin Kulla Alakar Kasar Da HKI
  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
  • Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata
  • Hukumar Birnin Istambul Ta Dakatar Da Akram Imamoglu Daga Matsayinsa Na Magajin Garin Birnin