Aminiya:
2025-04-13@11:06:06 GMT

Osimhen ya maka ɗan jarida a kotu

Published: 2nd, February 2025 GMT

Ɗan wasan gaba na tawagar Super Eagles ta Nijeriya da ke buga wasa a ƙungiyar Galatasaray Victor Osimhen, ya shigar da ƙarar wani ɗan jaridar Turkiya Tolga Bozduman bisa zargin ɓata masa suna.

A cikin wani saƙo da wani makusancin Osimhen ya wallafa a shafinsa na X, ya ce za a fara sauraron ƙarar da ɗan wasan ya shigar bayan da ɗan jaridan ya zarge shi da naushin sa.

Wannan dai na zuwa ne bayan da ɗan jarida Bozduman ya zargi Osimhe da cin zaraginsa, bayan tashi wasa 3-3 tsakanin ƙungiyarsa ta Galatasary da kuma Dynamo Kyiv.

Yanzu haka dai Osimhen na fuskantar bincike kan lamarin, kuma ana ci gaba da ce-ce-ku-ce a kai.

A makon da ya gabata ne dai dama labarin naushin ɗan jaridan ya fito, inda rahotanni suka nuna cewar Osimhen ya nemi ya bai wa ɗan jaridan kuɗi don ya goge hoton amma ya ƙi amincewa.

Osimhen mai shekaru 26 ya ƙaryata dukkanin zarge-zargen da ake masa, inda ya ce ya garzaya kotu ne don ya wanke kansa daga yunƙurin ɓata masa suna.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Jarida

এছাড়াও পড়ুন:

 Nigeria: Wani Bom Da Ya Tashi A Maiduguri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 7

Rahotanni da suke fitowa daga Nigeria sun ce, a kalla mutane 7 su ka rasa rayukansu, yayin da wasu da dama su ka jikkata sanadiyyar fashewar wasu abubuwa masu karfi akan hanyar Damboa-Zuwa Maiduguri.

Rahotannin sun ce abubuwan su fashe ne dai a lokacin da wasu ayarin motoci da suke wucewa ta hanyar tare da rakiyar sojoji a jiya Asabar da hakan ya haddasa asarar rayuka da kuma jikka.

Hanyar Damboa zuwa Maiduguri tana zuwa kananan hukumomi da dama a kudancin Jahar ta Borno, a lokaci daya kuma yanki ne da ya yi kaurin suna a matsayin matsugunin ‘yan Bokoharam.

An dade da rufe hanyar saboda matsalar tsaro, amma gwamnatin Babagana zulum ta sake bude ta, da kuma dawo da zirga-zirgar ababen hawa zuwa Damboa,Chibok da kuma wasu kananan hukumomi da suke a kudancin Jahar.

Ana barin matafiya su bi ta hanyar ne sai biyu a mako daya, bayan sojoji sun yi sintiri da kuma tabbatar da cewa ba a dasa abubuwan fashewa ba. Kusan shekaru biyu kenan ana yin haka. Tuni dai aka dauki wadanda su ka jikkata da ba a tantance adadinsu ba zuwa asibitin cikin Maiduguri domin yi musu magani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Nigeria: Wani Bom Da Ya Tashi A Maiduguri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 7
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassa Al-Mujtaba (a) 107
  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi
  • ’Yan bindiga sun harbi alkali da ɗansa, sun sace mutane 13 a Katsina
  • Mai damfarar fursunoni ya gurfana a kotu a Kano
  • ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja
  • Sudan ta kai karar Hadaddiyar Daular Larabawa a Kotun ICJ