A jiya Asabar kasar Amurka ta sanar da kakaba karin harajin kwastam na kaso 10% kan kayayyakin da kasar Sin take fitarwa zuwa Amurka. Dangane da batun, ma’aikatar kasuwanci ta Sin ta bayyana rashin jin dadi da kin amincewa daga bangaren Sin.

Cikin sanarwar da ma’aikatar ta gabatar, ta ce matakin Amurka ya keta ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya WTO, wanda ba zai ba da damar daidaita matsalar da kasar Amurka ke fuskanta ba, maimakon haka, zai lalata huldar hadin gwiwa tsakanin kasashen 2 ta fuskar tattalin arziki da cinikayya.

Ban da haka, ma’aikatar kasuwanci ta Sin ta ce, kasar Sin za ta kai kara ga kungiyar cinikayya ta duniya, da daukar matakai don mayar da martani ga matakin Amurka.

A sa’i daya kuma, kasar Amurka ta ce za ta sanya karin harajin kwastam da ya kai kaso 25%, kan kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen Mexico da Canada. Ban da haka, shugaban kasar Donald Trump ya ce yana duba yiwuwar kakaba karin haraji kan kayayyakin da ake shigar da su kasar Amurka daga kasashen Turai, ganin yadda kungiyar kasashen Turai EU ta hana shigowar motoci da amfanin gona na kasar Amurka cikin kasuwannin kasashen Turai, a lokacin da ya yi hira da ‘yan jaridu a kwanan baya. (Bello Wang)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran

Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Iran da kuma Amurka.

Kasar Iraki ta bayyana fatan tattaunawar za ta aifar da kwanciyar hankali a yankin

Ministan harkokin wajen Iraki ya bayyana goyon bayansa ga tattaunawar tsakanin Iran da Amurka, yana mai bayyana fatan Bagadaza na ganin cewa hakan zai samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Iraki ta fitar ta ce “Hussein ya karbi bakuncin mataimakin ministan harkokin wajen Iran Saeed Khatibzadeh a ranar Juma’a a gidansa da ke birnin Antalya na Turkiyya.

Sanarwar ta kara da cewa “a yayin ganawar, an tattauna dangantakar da ke tsakanin kasashen dake makobtaka da juna da kuma hanyoyin karfafa su a fannoni daban-daban.”

“Hussein ya yi maraba da tattaunawar ta tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Amurka, yana mai bayyana fatansa na cewa a wannan shawarwarin za a samu sakamako mai kyau da zai taimaka wajen samun kwanciyar hankali a yankin.”

Shi ma babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA Rafael Grossi ya bayyana fatansa na ganin an cimma yarjejeniyar nukiliyar tsakanin Iran da Amurka cikin gaggawa.

Grossi ya ce yana da kwarin gwiwar cewa bangarorin biyu za su iya warware sabanin ra’ayi a fannin tattalin arziki da cinikayya ta hanyar yin shawarwari kafada-da-kafada da hadin gwiwa don cin moriyar juna.

Stephane Dujarric, mai magana da yawun babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya bayyana fatansa game da tattaunawar ta tsakanin Amurka da kuma Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Matakin Kare-Karen Harajin Fito Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar
  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO