Aminiya:
2025-03-26@11:09:53 GMT

Fasinjoji 30 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Ondo

Published: 2nd, February 2025 GMT

Aƙalla fasinjoji 30 ne suka ƙone ƙurmus a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan titin Ore-Lagos a Jihar Ondo, bayan da wasu motoci biyu suka yi karo da juna sannan suka kama wuta.

Ganau, sun ce motocin suna tafiya zuwa Gabashin Najeriya ne, kuma suna gudun wuce ƙima kuma ga cunkoson ababen hawa a hanyar.

Osimhen ya maka ɗan jarida a kotu Abba ya karrama fitattun Kanawa 35

Hatsarin ya haddasa tashin wuta, inda mafi yawan fasinjojin suka ƙone ƙurmus.

“Motocin biyu sun yi karo, nan take suka kama da wuta,” in ji wata ganau, Misis Precision Oluwatuyi.

“Direbobin suna tafiya da gudu a hanyar da ba ta dace ba. Na ƙirga gawarwakin mutum 28 a waje , kuma wasu mutum biyu sun mutu a hanyarsu ta zuwa asibiti.”

Shugaban Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), Kwamanda Samuel Ibitoye, ya tabbatar da aukuwar hatsarin.

Ya ce sakaci da gudun wuce ƙima ne ya haddasa hatsarin.

“Direbobi su tuna cewa nauyin da ke kansu shi ne su kai fasinjoji inda za su je lafiya, ba su jefa rayuwarsu cikin hatsari ba,” in ji shi.

“Fasinjoji su ma su dinga gargaɗin direbobi kan tuƙin ganganci don kaucewa irin waɗannan musifu.”

An kai gawarwakin mamatan Asibitin Ƙasa da ke Ore, yayin da sauran mutum biyu da suka jikkata ake kula da su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hatsarin mota Ƙonewa

এছাড়াও পড়ুন:

Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul

Yansanda a kasar Turkiyya suna ci gaba da fafatawa day an adawa masu goyon bayan magajin garin birnin Istambul Ekram Imam oglu.

Tashar talabijin ta Al-mayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa magajin garin na birnin Istambul yana daga cikin fitattun masu adawa da gwamnatin Urdugan, sannan a halin yanzu jami’an sharia a kasar sun bada sanarwan cewa sun kammala bincike a kansa, kuma nan ba da dadewa ba zasu gurfanar da shi a gaban kotu don fuskantar shari’a.

A ranar laraban da ta gabat ce gwamnatin kasar Turkiya ta bada umurnin kama Ekram Imam oglu magajin garin birnin Istambul tare da zarginsa da cin hanci da rashawa da kuma ayyukan ta’addanci. Wanda ya musanta hakan a yanke.

Har’ila yau masu gabatar da shari’a a kasar sun bukaci a ci gaba da tsare magajin garin har zuwa lokacinda za’a fara shari’arsa a cikin yan kwanaki masu zuwa. Tun ranar laraban da ta gabace yan sanda a birnin istambul da kuma wasu birane a kasar suke fafatawa da dubban daruruwan magoya bayan Imam oglu wadanda suke bukatar a sake shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobarar daji ta kashe mutum 24 a Koriya ta Kudu
  • Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea
  • Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul
  • Kiyaye Ci Gaba Mai Dorewa A Huldar Sin Da Amurka Ya Dace Da Moriyar Sasssan Biyu
  • Matasa Sun Daka Wawasu Kan Tirelar Kayan Agajin Ramadan Na Seyi Tinubu A Gombe 
  • Dokar Ta-ɓaci A Ribas: Gwamnonin PDP Sun Ƙalubalanci Hukuncin Tinubu A Kotun Ƙoli
  • Ɗansanda Ya Kashe Matar Abokin Aikinsa, Ya Jikata Wasu Biyu A Ribas
  • Duniya na ci gaba da yin tir da Isra’ila kan dawo da hare-harenta a Gaza
  • UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya