Fasinjoji 30 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Ondo
Published: 2nd, February 2025 GMT
Aƙalla fasinjoji 30 ne suka ƙone ƙurmus a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan titin Ore-Lagos a Jihar Ondo, bayan da wasu motoci biyu suka yi karo da juna sannan suka kama wuta.
Ganau, sun ce motocin suna tafiya zuwa Gabashin Najeriya ne, kuma suna gudun wuce ƙima kuma ga cunkoson ababen hawa a hanyar.
Hatsarin ya haddasa tashin wuta, inda mafi yawan fasinjojin suka ƙone ƙurmus.
“Motocin biyu sun yi karo, nan take suka kama da wuta,” in ji wata ganau, Misis Precision Oluwatuyi.
“Direbobin suna tafiya da gudu a hanyar da ba ta dace ba. Na ƙirga gawarwakin mutum 28 a waje , kuma wasu mutum biyu sun mutu a hanyarsu ta zuwa asibiti.”
Shugaban Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), Kwamanda Samuel Ibitoye, ya tabbatar da aukuwar hatsarin.
Ya ce sakaci da gudun wuce ƙima ne ya haddasa hatsarin.
“Direbobi su tuna cewa nauyin da ke kansu shi ne su kai fasinjoji inda za su je lafiya, ba su jefa rayuwarsu cikin hatsari ba,” in ji shi.
“Fasinjoji su ma su dinga gargaɗin direbobi kan tuƙin ganganci don kaucewa irin waɗannan musifu.”
An kai gawarwakin mamatan Asibitin Ƙasa da ke Ore, yayin da sauran mutum biyu da suka jikkata ake kula da su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hatsarin mota Ƙonewa
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Shirin Sakin Dukkanin Fursunonin Isra’ila Bisa Sharuddan Da Ta Gindaya
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta sanar da sharudan sakin dukkan fursunonin Isra’ila da take tsare da su
Wani jami’in Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya ce: Kungiyar a shirye take ta sako daukacin fursunonin Isra’ila domin tsagaita bude wuta da ficewa daga Gaza, kamar yadda wani rahoto da tashar talabijin ta Alkahira ta fitar.
Jami’in na kungiyar Hamas ya kara da cewa: A ranar litinin din nan ne haramtacciyar kasar Isra’ila ta ci gaba da kawo cikas ga yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma yin watsi da alkawurran da ta dauka, yana mai cewa kungiyar Hamas ta tabbatar wa masu shiga tsakani da “bukatar bayar da lamuni don tilastawa gwamnatin mamayar Isra’ila aiwatar da yarjejeniyar.”
Yana mai bayyana cewa, “Hamas ta yi aiki mai kyau kuma tare da babban sassauci gami da aiki da ra’ayoyin da aka gabatar mata a cikin shawarwarin tsagaita wuta da musayar fursunonin Isra’ila.”