Aminiya:
2025-04-16@15:43:41 GMT

Fasinjoji 30 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Ondo

Published: 2nd, February 2025 GMT

Aƙalla fasinjoji 30 ne suka ƙone ƙurmus a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan titin Ore-Lagos a Jihar Ondo, bayan da wasu motoci biyu suka yi karo da juna sannan suka kama wuta.

Ganau, sun ce motocin suna tafiya zuwa Gabashin Najeriya ne, kuma suna gudun wuce ƙima kuma ga cunkoson ababen hawa a hanyar.

Osimhen ya maka ɗan jarida a kotu Abba ya karrama fitattun Kanawa 35

Hatsarin ya haddasa tashin wuta, inda mafi yawan fasinjojin suka ƙone ƙurmus.

“Motocin biyu sun yi karo, nan take suka kama da wuta,” in ji wata ganau, Misis Precision Oluwatuyi.

“Direbobin suna tafiya da gudu a hanyar da ba ta dace ba. Na ƙirga gawarwakin mutum 28 a waje , kuma wasu mutum biyu sun mutu a hanyarsu ta zuwa asibiti.”

Shugaban Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), Kwamanda Samuel Ibitoye, ya tabbatar da aukuwar hatsarin.

Ya ce sakaci da gudun wuce ƙima ne ya haddasa hatsarin.

“Direbobi su tuna cewa nauyin da ke kansu shi ne su kai fasinjoji inda za su je lafiya, ba su jefa rayuwarsu cikin hatsari ba,” in ji shi.

“Fasinjoji su ma su dinga gargaɗin direbobi kan tuƙin ganganci don kaucewa irin waɗannan musifu.”

An kai gawarwakin mamatan Asibitin Ƙasa da ke Ore, yayin da sauran mutum biyu da suka jikkata ake kula da su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hatsarin mota Ƙonewa

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Shirin Sakin Dukkanin Fursunonin Isra’ila Bisa Sharuddan Da Ta Gindaya

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta sanar da sharudan sakin dukkan fursunonin Isra’ila da take tsare da su

Wani jami’in Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya ce: Kungiyar a shirye take ta sako daukacin fursunonin Isra’ila domin tsagaita bude wuta da ficewa daga Gaza, kamar yadda wani rahoto da tashar talabijin ta Alkahira ta fitar.

Jami’in na kungiyar Hamas ya kara da cewa: A ranar litinin din nan ne haramtacciyar kasar Isra’ila ta ci gaba da kawo cikas ga yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma yin watsi da alkawurran da ta dauka, yana mai cewa kungiyar Hamas ta tabbatar wa masu shiga tsakani da “bukatar bayar da lamuni don tilastawa gwamnatin mamayar Isra’ila aiwatar da yarjejeniyar.”

Yana mai bayyana cewa, “Hamas ta yi aiki mai kyau kuma tare da babban sassauci gami da aiki da ra’ayoyin da aka gabatar mata a cikin shawarwarin tsagaita wuta da musayar fursunonin Isra’ila.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda
  • Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Shirin Sakin Dukkanin Fursunonin Isra’ila Bisa Sharuddan Da Ta Gindaya
  • Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • Sojoji Sun Ceto Fasinjoji 16 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Filato
  • Mutum 45 Sun Rasa Rayukansu A Wani Sabon Hari A Filato 
  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran