La’anannen dan siyasar Sweden din nan mai kyamar addinin Islama, Rasmus Paludan, ya sake tozarta kur’ani mai tsarki a birnin Copenhagen na kasar Denmark.

Paludan mai shekaru 43 shugaban jam’iyyar adawa ta kasar Denmark Stram Kurs, ya sake haifar da cece-kuce ta hanyar aikata wannan aika aika a wajen ofishin jakadancin Turkiyya da ke Denmark.

Wani faifan bidiyo da aka watsa a dandalin sada zumunta ya nuna Paludan yana wulakanta kur’ani mai tsarki, matakin da ya yi matukar bakanta ran musulmin duniya.

Matakin na Paludan ya zo ne bayan kisan da aka yi wa wani dan kasar Iraki mai suwan Salwan Momika wanda ya walakanta Al’Kur’ani a gidansa da ke birnin Sodertalje a ranar 30 ga watan Janairu.

Matashin mai shekaru 38 da haifuwa ya gudanar da kone-kone da tozarta littafin na Islama da dama a kasar Sweden a shekarar 2023.

Shi ma Paludan, ya shahara da tsokanar addinin musulmi ta hanyar kona kwafin kur’ani mai tsarki a kasashen Sweden da Denmark.

Kotun birnin Copenhagen a ranar 22 ga watan Nuwamban shekarar da ta gabata ta yanke wa dan siyasar mai ra’ayin rikau hukunci bayan ta same shi da laifin nuna wariyar launin fata dangane da furucin da ya yi yayin wata zanga-zanga a shekarar 2019.

A farkon wannan watan ne aka yanke wa Paludan hukuncin daurin watanni hudu a gidan yari a kasar Sweden saboda laifin yin batanci ga musulmi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran

Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana alhininsa akan rasuwar Dr. Akbar I’itimadi wanda shi ne na farko da ya kafa hukumar makamashin Nukiliya ta Iran.

Wasikar ta’aziyyar da shugaban kasa ta kunsa ta ambaci cewa:  Shakka babu hidima mai kima da wannan masanin ya yi, ya share fagen gina da ci gaban fasahar makamashin Nukiliya a Iran da kuma mayar da kasar mai cin gashin kanta a wannan fage.

Har ila yau, shugaban kasar ta Iran ya mika sakon ta’aziyyarsa ga masana na Iran, da kuma iyalansa. Ya kuma yi addu’a da rokon Allah madaukin sarki da ya lullube shi da rahamarsa da kuma gafararsa, sannan ya bai wa iyalansa na hakuri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi: babu tattaunawa kan batun tace sinadarin uranium
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
  • NNPP Ta Mutu, Kwankwaso Zai Sake Dawowa APC – Ganduje
  • Jagoran Ya Ce: Iran Ba Ta Kallon Tattaunawan Iran Da Amurka A Matsayin Kawo Karshen Takaddama A Tsakaninsu
  • Rasha Ta Sanar Da Kashe Manyan Kwamandojin Sojin Ukraine Fiye Da 60 A Birnin Sumy Na Kasar Ta Ukraine
  • Hauhawar Farashi ya ƙaru a watan Maris — NBS
  • Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC
  • Kasashen Da Mata Ba Su Taba Mulki Ba A Tarihi
  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya