Rahoto : Amurka Na Matsin Lamba Wa Ukraine Ta Gudanar Da Zabe Zuwa Karshen Shekara
Published: 2nd, February 2025 GMT
Rahotanni sun ce gwamnatin shugaban Amurka Donald Trump na matsawa kasar Ukraine lamba domin gudanar da zabuka a karshen wannan shekara a daidai lokacin da ake kokarin kulla yarjejeniyar sulhu tsakanin Kiev da Moscow.
Wakilin Trump na musamman kan Ukraine da Rasha, Keith Kellogg, ya fada a wata hira da ya yi da kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin Ukraine da aka dakatar a yakin da ake yi da Rasha, suna bukatar a gduanar da su.
“Yawancin kasashen dimokuradiyya suna gudanar da zabe a lokacin yakinsu. Ina ganin yana da mahimmanci su yi haka,”in ji Kellogg.
Kamfanin dillancin labaran reuters ma ya rawaito wasu jami’an fadar White House sun tattauna batun matsawa Ukraine ta amince da gudanar da zabe a wani bangare na duk wata yarjejeniya ta farko da Rasha.
Trump da Kellogg sun ce suna aiki kan wani shiri na shiga tsakani a cikin watannin farko na sabuwar gwamnatin Amurka don kawo karshen yakin da ya barke a watan Fabrairun 2022.
Har yanzu dai ba a fayyace shirin ba kuma har yanzu ba a san yadda za a karbi shirin a cikin kasar Ukraine domin kawo karshen rikicin mafi muni a Turai tun bayan yakin duniya na biyu.
A baya shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskyy ya ce Kiev za ta iya gudanar da zabe a wannan shekara idan fadan ya kare da kuma samar da kwakkwaran tabbacin tsaro ga Ukraine.
A cikin shekarar 2024 ne wa’adin shekaru biyar na Zelensky ya kamata ya kare amma ba’a iya gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisa a karkashin dokar soja ba, wanda Ukraine ta sanya a watan Fabrairun 2022.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Haren Kan Wasu Wurare A Gabaci Da Kuma Kudancin Kasar Lebanon
Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare a gabaci da kuma kudancin kasar Lebanon wanda yak eta yarjeniyar zaman lafiyan da HKI ta cimma da kungiyar Hizbullah mai lamba 1701 ta shekara ta 2006.
Tashar talabijin ta Presstv anan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran gwamnatin kasar Lebanon na cewa, jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan bayan kauyen taraya a gundumar ba’alabak, cikin lardin Ba’alabak Hermel, da kuma kan garin Shaara kusa da garin Jenta a dai dai kasar tsaunuka da ke yankin.
A kudancin kasar Lebanon kuma jiragen yakin HKI sun jefa makamai masu linzami har guda 4 a kan yakunan Jibaa da Snaya
Kafafen yada labaran HKI sun tabbatar da wannan labarin sun kuma nakalto sojojin kasar suna cewa sun kai hare-haren ne kan damdamalin cilla makamai masu linzami na kungiyar Hizbullah.
Sanarwan sojojin yahudawan ya ce: Sojojin HKI sun kai hari kan wuraren kungiyar Hizbullah, wadanda suke karkashin kasa a lardin Biqaa a kasar Lebanon.
Gwamnatin HKI a dole ta amince da tsagaita budewa juna wuta da kungiyar Hizbullah a ranar 27 ga watan Nuwamban shekarar da ta gabata, bayan asarorin na rayukan sojoji da tankunan yaki da kuma gine-gine masu muhimmanci wadanda kungiyar Hizbullah ta lalata a cikin yakin watanni 14 da suka fafata. Ta amince da kuduri kwamitin tsaro mai lamba 1701 na kwamitin tsaro ba tare da ta cimma ko guda daga cikin manufofin fara yakin ba.