Rahoto : Amurka Na Matsin Lamba Wa Ukraine Ta Gudanar Da Zabe Zuwa Karshen Shekara
Published: 2nd, February 2025 GMT
Rahotanni sun ce gwamnatin shugaban Amurka Donald Trump na matsawa kasar Ukraine lamba domin gudanar da zabuka a karshen wannan shekara a daidai lokacin da ake kokarin kulla yarjejeniyar sulhu tsakanin Kiev da Moscow.
Wakilin Trump na musamman kan Ukraine da Rasha, Keith Kellogg, ya fada a wata hira da ya yi da kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin Ukraine da aka dakatar a yakin da ake yi da Rasha, suna bukatar a gduanar da su.
“Yawancin kasashen dimokuradiyya suna gudanar da zabe a lokacin yakinsu. Ina ganin yana da mahimmanci su yi haka,”in ji Kellogg.
Kamfanin dillancin labaran reuters ma ya rawaito wasu jami’an fadar White House sun tattauna batun matsawa Ukraine ta amince da gudanar da zabe a wani bangare na duk wata yarjejeniya ta farko da Rasha.
Trump da Kellogg sun ce suna aiki kan wani shiri na shiga tsakani a cikin watannin farko na sabuwar gwamnatin Amurka don kawo karshen yakin da ya barke a watan Fabrairun 2022.
Har yanzu dai ba a fayyace shirin ba kuma har yanzu ba a san yadda za a karbi shirin a cikin kasar Ukraine domin kawo karshen rikicin mafi muni a Turai tun bayan yakin duniya na biyu.
A baya shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskyy ya ce Kiev za ta iya gudanar da zabe a wannan shekara idan fadan ya kare da kuma samar da kwakkwaran tabbacin tsaro ga Ukraine.
A cikin shekarar 2024 ne wa’adin shekaru biyar na Zelensky ya kamata ya kare amma ba’a iya gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisa a karkashin dokar soja ba, wanda Ukraine ta sanya a watan Fabrairun 2022.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
Wani matashi ɗan shekara 18 mai suna Bakura Muhammed, ya gamu da ajalinsa a wani rikici da ya ɓarke tsakanin ƙungiyoyin matasa masu gaba da juna da ake wa laƙabi da Malians a Maiduguri.
Majiyoyin leken asiri sun shaida wa Zaga-zola Makama cewa, rikicin ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yammacin ranar 4 ga watan Afrilun nan a yankin Ajari da Tashar Lara, inda matasan ɓangarorin biyu suka yi artabu da juna.
An daɓa wa wanda aka kashen wuƙa a ciki, wanda ba tare da ɓata lokaci ba jami’an tsaro na Maidugurin suka ɗauke shi zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri, inda jami’an lafiya suka tabbatar da rasuwarsa.
Wata majiyar ‘yan sanda ta ce, an kama wasu mutane bakwai masu shekaru tsakanin 15 zuwa 24.
Majiyar ta bayyana sunayen ababen zargin da aka kama da suka haɗa da Ba’abba Kyari mai kimanin shekara 20 sai Ali Alhaji Goni Ali dan shekara 20 da Muhammed Audu mai kimanin shekara 18, sai Ali Isa mai shekara 15 da Adam Sabir mai shekara 15 da Mohammed Tujja shekaru 17 da Usman Kasim dan shekara 24