Hamas Ta Yi Tir Da Shawarar Shugaban Amurka Ta Kwashe Falasdinawa Daga Gaza
Published: 2nd, February 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta yi Allah-wadai da kalaman shugaban Amurka Donald Trump kan mayar da mazauna Gaza zuwa kasashen Masar da Jordan dake makwabtaka da ita.
A cikin wata sanarwar da ya fitar, shugaban kungiyar Hamas Sami Abu Zuhri ya yi tir da irin wadannan shawarwari a matsayin “abin dariya kuma maras amfani,” yana mai cewa, “Abin da mamayar Isra’ila ta kasa cimma da karfi, ba zai samu ta hanyar makircin siyasa ba.
Abu Zuhri ya kara da cewa, “Sanarwar da Amurka ta nanata na raba Falasdinawa da gidajensu da nufin sake gina yankin zirin Gaza na nuni da yadda kasar ke da hannu wajen aikata laifukan da suka shafi yanki.”
Kana, ya yi gargadin cewa, “aikin kwashe mazauna Gaza” wani makirci ne na kara hargitsi da tashin hankali a yankin.
A ranar 25 ga watan Janairu ne dai Trump ya gabatar da wannan tsari mai cike da cece-kuce na kwashe Falasdinawa daga Gaza zuwa Masar da Jordan, wanda kasashen biyu suka ki amincewa da shi matuka.
Shi dai Shugaban Amurka Donald Trump ya jaddada kiransa ga kasashen Masar da Jordan domin su karbi Falasdinawan Gaza da suka rasa matsugunansu, duk da cewa kasashen Larabawan biyu sun yi watsi da shawararsa da ke cike da ce-ce-ku-ce.
Haka su ma kasashen Qatar, UAE da kuma Saudiyya sun yi fatali da shawarar da Trump ya bayar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran da Amurka na shirin tattaunawa ta biyu a birnin Rome
Yau Asabar Washington da Tehran, ke tattauanwa a birnin Rome na kasar Italiya, wace ita ce ta biyu a shiga tsakanin kasar Oman kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
Tattaunwar wacce ba ta gaba-da-gaba ba an gudanar da irin ta a ranar Asabar data gabata a birnin Muscat na kasar Oman, inda bangarorin biyu suka bayyana tattaunawar da mai armashi.
Gabanin tattaunawar ta yau, Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce akwai yuwuwar kulla yarjejeniya da Amurka idan har Washington ba ta gabatar da wasu bukatu na da suka wuce da tunani ba”.
Araghchi ya bayyana hakan ne a yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa da takwaransa na Rasha, Sergei Lavrov, a ranar Juma’a a birnin Moscow, gabanin tattaunawar ta biyu tsakanin Tehran da Washington, da ake shirin gudanarwa yau a birnin Rome na kasar Italiya.
“Za mu tattauna kan batun nukiliya ne kawai, kuma ba za a saka wasu batutuwa a cikin wannan tattaunawar ba,” in ji shi.
Ya kara da cewa “Ina ganin mai yiyuwa ne a cimma matsaya idan [Amurkawa] suka nuna da gaske su ke kuma ba su gabatar da bukatu da ba su dace ba.
Sai dai ya jaddada cewa: “Hanyar diflomasiya a bude take, amma ya nuna matukar shakku game da aniyar Amurka idan aka yi la’akari da matsayin Washington da ke cin karo da juna.
“Muna da matukar shakku game da aniya da manufar bangaren Amurka, amma za mu shiga shawarwarin tare da azama.”Ya kuma jaddada aniyar Tehran ta ci gaba da samar da hanyoyin warware shirinta na nukiliya cikin lumana.