HausaTv:
2025-02-22@06:34:49 GMT

Hamas Ta Yi Tir Da Shawarar Shugaban Amurka Ta Kwashe Falasdinawa Daga Gaza

Published: 2nd, February 2025 GMT

Kungiyar Hamas ta yi Allah-wadai da kalaman shugaban Amurka Donald Trump kan mayar da mazauna Gaza zuwa kasashen Masar da Jordan dake makwabtaka da ita.

A cikin wata sanarwar da ya fitar, shugaban kungiyar Hamas Sami Abu Zuhri ya yi tir da irin wadannan shawarwari a matsayin “abin dariya kuma maras amfani,” yana mai cewa, “Abin da mamayar Isra’ila ta kasa cimma da karfi, ba zai samu ta hanyar makircin siyasa ba.

Abu Zuhri ya kara da cewa, “Sanarwar da Amurka ta nanata na raba Falasdinawa da gidajensu da nufin sake gina yankin zirin Gaza na nuni da yadda kasar ke da hannu wajen aikata laifukan da suka shafi yanki.”

Kana, ya yi gargadin cewa, “aikin kwashe mazauna Gaza” wani makirci ne na kara hargitsi da tashin hankali a yankin.

A ranar 25 ga watan Janairu ne dai Trump ya gabatar da wannan tsari mai cike da cece-kuce na kwashe Falasdinawa daga Gaza zuwa Masar da Jordan, wanda kasashen biyu suka ki amincewa da shi matuka.

Shi dai Shugaban Amurka Donald Trump ya jaddada kiransa ga kasashen Masar da Jordan domin su karbi Falasdinawan Gaza da suka rasa matsugunansu, duk da cewa kasashen Larabawan biyu sun yi watsi da shawararsa da ke cike da ce-ce-ku-ce.

Haka su ma kasashen Qatar, UAE da kuma Saudiyya sun yi fatali da shawarar da Trump ya bayar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila-Hamas: Za’ayi Musayar Fursunonin Karshe Karkashin Yarjejeniyar Farko

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta ca zata saki ‘yan Isra’ila shida yau Asabar a matakin karshe na yarjejeniyar tsagaita wuta ta farko da ta cimma da Isar’ila.

An kuma tsara Isra’ila za ta saki fursunonin falasdinawa Falasdinawa 602 a wannan Asabar a musayar wacce ita ce ta bakwai tun cimma yarjejeniyar a ranar 19 ga watan Janairu tsakanin Isra’ila da Hamas.

Tun dai bayan cimma yarjejeniyar Hamas ta saki Isra’ilawa 22, a yayin da ita kuwa Isra’ila ta saki fursunonin Falasdinawa sama da 1,100.

A karshen matakin farko na yarjejeniyar tsagaita bude wuta, za a yi musayar fursunonin Falasdinawa 1,900 da aka yi garkuwa da ‘yan Isra’ila  su 33 da suka hada da matattu takwas.

Ana dai ci gaba da tattaunawa kan mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wutar tsakanin bangarorin biyu a yayin da dukkansu ke zargin juna da keta yarjejeyar.

Shugaban ofishin yada labarai na gwamnati a Gaza ya sanar da cewa sau fiyesama da 350 Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita da Isra’ila ta cim ma a ranar 15 ga watan Janairu.

Tun bayan sanya hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta, sojojin Isra’ila sun kashe tare da raunata Falasdinawa da dama ta hanyar hare-hare ta sama da suka hada da jiragen yaki da jirage marasa matuka, da harbe-harbe kai tsaye.

Sauran laifukan sun hada da kutsen da Isra’ila ta yi a yankunan kan iyaka da ke gabashin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila-Hamas: Za’ayi Musayar Fursunonin Karshe Karkashin Yarjejeniyar Farko
  • Thomas Friedman: Trump Yana Son Ci Gaba Da Zama Shugaban Kasar Amurka Har Abada
  • Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Suke Da Hakkin Yanke Shawarar Makomar Kaarsu Ba Amurka Ba
  • Saudiyya ta Gayyaci Kasashen Larabawa Kan Batun Kan Batun Gaza
  • Palasdinawa Ne Zasu Fayyanace Makomarsu Ba Wasu Dan Mulkin Mallaka Ba: Qalibof
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Watsi Da Karin Shuruddan Gwamnatin ‘Yan Sayoniyya Kan Tsagaita Bude Wuta
  • Kasashen Rasha Da Amurka Sun Kuduri Anniyar Kawo Karshen Yaki A Ukraine