Sakatare Janar na kungiyar Hizbullah ta Lebanon Sheikh Naim Qasem ya ce gwamnatin Lebanon ce ke da alhakin tabbatar da cewa Isra’ila ta mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a kasar ta Lebanon.

“Gwamnatin Lebanon, bayan tsawaita yarjejeniyar tsagaita bude wuta, ita ce ke da alhakin bibiyar lamarin da kuma matsa lamba kan kasashe masu sa ido da masu shiga tsakani don dakatar da hare-haren da Isra’ila ke kaiwa da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta,” in ji shi a wani jawabi da ya yi ta gidan talabijin dazu.

Sheik Qasem ya ce kungiyar Hizbullah na taka-tsan-tsan don bai wa gwamnatin Lebanon damar sauke nauyin da ya rataya a wuyanta karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Faransa da Amurka suka shiga tsakani a ranar 27 ga watan Nuwamba.

Ya yi gargadin cewa Isra’ila na ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

Ya kamata Isra’ila ta janye dukkan sojojinta daga Lebanon a ranar 26 ga watan Janairu a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta da ta rattabawa hannu da kungiyar Hizbullah a watan Nuwamba.

Sai dai kuma ta ki yin hakan, inda aka tsawaita wa’adin zuwa ranar 18 ga watan Fabrairu.

Sama da ‘yan kasar Lebanon 80 ne kuma aka kashe a hare-haren da Isra’ila ke kaiwa kasar tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta fara aiki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita bude wuta

এছাড়াও পড়ুন:

 Aljeriya Ta Kori Jami’an Diflomasiyya Faransa 12

Gwamnatin kasar Ajeriya ta bayyana jami’an diflomasiyyar Faransa da suke kasar su 12 a matsayin ‘wadanda ba a bukatar ganinsu” a cikin kasar, tare da yin kira a gare su da su fice a cikin sa’oi 48.

Bugu da kari kasar ta Aljeriya ta yi suka da kakkausar murya akan ministan harkokin wajen Faransa Bruno Rotayo,tare da cewa za ta mayar masa da martanin da ya dace.

Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Aljeriya ta bayyana cewa; A matsayinta na kasa mai cikakken shugabanci, tana daukar ma’aikatan ofishin jakadanci Faransa 12 a matsayin wadanda ba a maraba da su, sannan kuma ana bukatar da su fice daga kasar a cikin sa’oi 48.”

 Aljeriya din ta dauki wannan matakin ne a matsayin mayar da martani ga kama wani jami’in diflomasiyyarta da aka yi a kasar Faransa a ranar 8 ga watan Aprilu da ake ciki.

Aljeriyan ta bayyana abinda ya faru da cewa, keta hurumin kasarta ne da kuma take dokokin aikin diflomasiyya.”

Haka nan kuma ta yi ishar da cewa, ma’aikacin diflomasiyyar da aka kama yana da kariya ta aiki wacce ta hana a yi masa abinda ya faru,amma kuma gwamnatin Faransa ta yi mu’amala a shi ta hanya mafi muni da halayya irin ta barayi.’

Alaka a tsakanin Faransa da Aljeriya tana kwan-gaba da baya, musamman a cikin watannin bayan nan. Watanni 8 da su ka gabata an sami rashin jituwa a tsakaninsu saboda korar wasu ‘yan asalin Aljeriya mazauna Faransa bisa zargin cewa sun shiga kasar ba bisa ka’ida ba. Aljeriya ta yi wa jakadanta kiranye, tare da rufe kafar diflomasiyya a tsakaninsu na tsawon watanni 8.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Shirin Sakin Dukkanin Fursunonin Isra’ila Bisa Sharuddan Da Ta Gindaya
  • CMG Ta Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Gidan Talabijin Na Kasar Vietnam
  • Hauhawar Farashi ya ƙaru a watan Maris — NBS
  • EFCC ta gaza tabbatar da tuhumar Murja kan zargin wulaƙanta takardar Naira
  • Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC
  • Noman rake: Najeriya da China sun kulla yarjejeniyar kasuwancin $1bn
  • Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
  •  Aljeriya Ta Kori Jami’an Diflomasiyya Faransa 12
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • Jiragen Saman Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Luguden Wuta Kan Asibitin Baptist Da Ke Gaza