Qasem : Dole Ne Lebanon Ta Tabbatar Da Cewa Isra’ila Ta Aiwatar Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
Published: 2nd, February 2025 GMT
Sakatare Janar na kungiyar Hizbullah ta Lebanon Sheikh Naim Qasem ya ce gwamnatin Lebanon ce ke da alhakin tabbatar da cewa Isra’ila ta mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a kasar ta Lebanon.
“Gwamnatin Lebanon, bayan tsawaita yarjejeniyar tsagaita bude wuta, ita ce ke da alhakin bibiyar lamarin da kuma matsa lamba kan kasashe masu sa ido da masu shiga tsakani don dakatar da hare-haren da Isra’ila ke kaiwa da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta,” in ji shi a wani jawabi da ya yi ta gidan talabijin dazu.
Sheik Qasem ya ce kungiyar Hizbullah na taka-tsan-tsan don bai wa gwamnatin Lebanon damar sauke nauyin da ya rataya a wuyanta karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Faransa da Amurka suka shiga tsakani a ranar 27 ga watan Nuwamba.
Ya yi gargadin cewa Isra’ila na ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta.
Ya kamata Isra’ila ta janye dukkan sojojinta daga Lebanon a ranar 26 ga watan Janairu a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta da ta rattabawa hannu da kungiyar Hizbullah a watan Nuwamba.
Sai dai kuma ta ki yin hakan, inda aka tsawaita wa’adin zuwa ranar 18 ga watan Fabrairu.
Sama da ‘yan kasar Lebanon 80 ne kuma aka kashe a hare-haren da Isra’ila ke kaiwa kasar tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta fara aiki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita bude wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
Ministan harkokin wajen kasar Iran, Abbas Araghchi, ya yi kakkausar suka kan zaluncin da gwamnatin Isra’ila ke yi kan al’ummar Falasdinu da ba su da kariya a yankin Zirin Gaza, yana mai jaddada bukatar hadin kai da daukar matakin gaggawa na kasashen musulmi domin dakile wadannan laifuka.
Babban jami’in diflomasiyyar ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan a ranar Asabar, inda ya bukaci kasashen musulmi a duk fadin duniya da su dauki kwararen matakai da hadin kai don tunkarar ta’addancin Isra’ila.
Araghchi ya yi nuni da yadda gwamnatin Isra’ila ta sake dawo da yakin da take yi na kisan kare dangi a kan Gaza tun ranar Talatar data gabata wanda ya keta yarjejeniyar tsagaita bude wutar da aka cimma a zirin.
Sabon farmakin Isra’ila ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa sama da 1,000, akasari mata da yara, baya ga kusan mutane 48,000 da sojojin suka yi wa kisan kare dangi tun da farko.
A wani bangare na jawabin nasa, Araghchi ya yi tir da hare-haren wuce gona da iri da Amurka da Birtaniya ke yi kan kasar Yemen, inda ya bayyana irin asarar da aka yi a tsakanin mata da kananan yara da ba su ji ba ba su gani ba, da kuma lalata kayayyakin more rayuwa na kasar.
Ya jaddada nauyin daya rataya a wuyan al’ummar musulmin duniya na tallafa wa ‘yan uwansu a wannan kasa ta Larabawa mai fama da tashe-tashen hankula da talauci.
A nasa bangaren, Yarima Farhan ya nanata matsayar Riyadh na yin Allah wadai da mummunan zaluncin gwamnatin Isra’ila, Ya kuma jaddada wajabcin hada kai da hadin gwiwa a tsakanin kasashen yankin don hana barkewar rikicin.