Iran Ta Samu Ci Gaba A Kowane Fanni A Cikin Shekaru 40
Published: 2nd, February 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya yaba da ci gaban da Iran ta samu a fagage daban-daban, yana mai cewa kasar ta samu bunkasa a dukkan bangarori cikin shekaru 40 da suka gabata.
Iran ta yau ba Iran ce ta shekaru 40 da suka gabata ba – mun ci gaba ta kowane fanni,” in ji shi.
Jagoran ya jaddada cewa “Abin da ya bambanta Iran da sauran al’ummomi da yawa shi ne jajircewar mutanen kasar na yin Allah wadai da Amurka a matsayin mai zalunci, makaryaciya, mayaudariya da girman kai.”
Jagoran ya bayyana hakan ne a wata ganawa yau Lahadi tare da mahardatan musabaka ta Al’kur’ani mai tsarki karo na 41 da aka gudanar a Tehran babban birnin kasar Iran.
Har ila yau Ayatullah Khamenei ya jinjinawa irin sadaukarwar da kungiyoyin gwagwarmayar Falastinawa suke yi kan gwamnatin Isra’ila.
“In Allah ya yarda, Gaza za ta yi galaba a kan gwamnatin Sahayoniya,” in ji shi.
Ayatullah Khamenei ya jaddada nasarar da al’ummar Gaza suka samu kan gwamnatin sahyoniyawa da gwamnatin Amurka a matsayin misali na tabbatar da abin da ake ganin ba zai taba yiwuwa ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
A zantawa ta water tarho ministocin harkokin waje na kasashen Iran da Turkiya sun bukaci kasashen musulmi su magance matsalar jinkai da kayakin agaji na Falasdinawa a kasarsu da aka mamaye.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Hakan Fidan na kasar Turkiya da tokwaransa na kasar Iran Abbas Aragchi suna fadar haka a jiya Litinin.
A lokacinda yake Magana a kan rikicin da ke faruwa a kasar Turkiyya Abbas Aragchi ya bayyana cewa, rikici ne na cikin gida, kuma yana fatan gwamnatin kasar zara iya magancece ta yadda ta ga ya dace, kuma yana da imani zata iya magance matsalar.
Aragchi ya kara da cewa, wannan shi ne matsayin iran a cikin al-amuran da ke faruwa a kasashen yankin, ya kuma bayyana muhimmancin mutunta al-amuran da suka shafi cikin gida na ko wace kasa a yankin.
Sai kuma Hakan Fidan ministan harkokin wajen Turkiya wanda ya sake jadda matsayin kasarsa wajen neman hanyoyin diblomasiyya don warware matsalolin al-amuran Falasdinu da kasashen yankin da kuma sauran kasashen duniya.